Connect with us

Laifi

Ya binne ƙaninsa da rai, bayan ya yi masa duka, kan zarginsa da sata

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kogi ta kama wani matashi mai suna Goodness Oshodi mai shekaru 19 da haihuwa da ake zargin ya binne ƙaninsa mai suna Friday Oshhodi da ransa bisa zargin satar Naira 1000.

Lamarin ya faru ne da yammacin talata 10 ga watan Oktoba, 2023, a unguwar Apamisede, a ƙaramar hukumar Adavi ta jihar.

Sai dai wanda abin ya shafa ya yi sa’a da maƙwabta sun ceto shi.

A cewar shaidun gani da ido, mahaifiyar Goodness ta umarce shi da ya hukunta Friday bisa zargin satar mata Naira 1,000.

 An tattaro cewa Goodness ya lakaɗa wa Friday duka kafin ya binne shi da rai.

KU KUMA KARANTA: Ɗan fari ya kashe ɗan autansu da duka, ya raba kansa gida biyu

Da yake magana kan dalilin da yasa ya yanke shawarar binne ɗan uwansa da rai, Goodness ya ce yana aiwatar da umarnin mahaifiyarsu ne kawai da ta buƙaci ya hukunta ɗan uwansa bisa zargin satar mata Naira 1000 da ƙoƙarin gudu.

A cewarsa, mahaifiyar wadda ta umarce shi da ya hukunta Friday, ta je coci lokacin da ya binne shi da rai.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP William Aya, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce an kama yaron kuma ana yi masa tambayoyi.

“Eh, muna sane.  An kama yaron, ana ci gaba da gudanar da bincike kan dalilin da ya sa kuma ta yaya hakan zai iya faruwa,” PPRO ya ƙara da cewa.

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

An kashe wata ɗalibar jami’a mai shekaru 21 bayan an yaudareta da wasu kuɗi

Published

on

An kashe wata ɗalibar jami'a mai shekaru 21 bayan an yaudare ta da wasu kuɗi

An kashe wata ɗalibar jami’a mai shekaru 21 bayan an yaudareta da wasu kuɗi

Daga Ali Sanni Larabawa

Wata budurwar mai shekara 21 da aka bayyana ɓacewarta tun ranar 9 ga watan Agustan 2024, an same ta babu rai a wani wajen zubda shara dake unguwar Aleniboro a Ilorin, babban birnin jihar.

Rundunar ‘yan sandar jihar, ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Talata.

Kakakin rundunar, DSP Toun Ejire-Adeyemi, ya bayyana cewa marigayiyar ta samu ƙiran waya daga wata Mis Timileyin a ranar 9 ga watan Agusta, 2024, game da wani taron da ɗaliban makarantar a Offa, da suka shirya.

Matar ta gabatar da marigayiyar ga wani Mista Adebayo Happiness, ɗaliban Jami’ar Summit, wanda ake zargin ya gayyace ta zuwa liyafar dare a kan zargin cewa tayi a matsayin budurwarsa kan kuɗi naira 15,000.

KU KUMA KARANTA: An watsa wa budurwa tafasasshen man gyaɗa a fuska a Zariya

“Duk da haka, marigayiya Mojisola ta sanarwa da abokiyar zamanta, wata Blessing O, cewa ta ji ba dadi a otal ɗin da Adebayo Happiness ya sauƙe ta kuma ta lura cewa babu wani biki a wajen da aka ce.

“Ba daɗewa bayan wannan tattaunawar wayarta a kashe ta kuma duk ƙoƙarin da Miss Blessing ta yi na samunta baiyi nasara ba”, in ji shi.

Tace an kama wanda zake zargin aikata kisan kuma an miƙa shi ga cibiyar binciken laifuka ta jihar.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama wani ɓarawon mota

Published

on

'Yan sanda sun kama wani ɓarawon mota

‘Yan sanda sun kama wani ɓarawon mota

Daga Ali Sanni Larabawa

Rundunar ‘yan sandar babban birnin tarayyar Najeriya, sunyi nasarar kama wani mutum da ake zargi da ƙwace wata mota ta hanyar amfani da bindiga, watanni uku da suka wuce.

Kwamishinan ‘yan sandar Abuja, Benneth Igweh ne, ya bayyana hakan lokacin da yake gabatar da wanda ake zargi a ranar Litinin.

Ya ce wanda ake zargin, mai suna Michael Uke, ya sace mota ƙirar Toyota Corolla mai lamba ABC 258 LD ta hanyar amfani da bindiga a ranar 2 ga watan Mayu, 2024, a kan hanyar Kuje.

KU KUMA KARANTA: Wasu matasa a Bauchi sun ƙone ɓarayin adaidaita sahu har lahira

‘Yan sandan sun bi sawun sa har zuwa wani otal dake yankin Jabi, inda suka same shi tare da motar daya sace.

‘Yan sandan sun kuma gano cewa wanda ake zargin ya sauya lambar motar zuwa AGD 146 JP.

A yayin binciken, sun gano na’urar POS, wuƙa, da kuma hular sojoji a wajensa.

‘Yan sandan na cigaba da gudanar da bincike  a kan lamarin.

Rundunar ta buƙaci mazauna yankin su riƙa sanar da su abubuwan da ke faruwa ta waɗnnan lambobin: 08032003913, 08028940883, 08061581938, da 07057337653.

Continue Reading

Laifi

‘Yan bindiga a Kaduna sun kashe wani likita da sace mutane 8

Published

on

'Yan bindiga a Kaduna sun kashe wani likita da sace mutane 8

‘Yan bindiga a Kaduna sun kashe wani likita da sace mutane 8

Daga Ali Sanni Larabawa

‘Yan bindiga sun kashe wani likita tare da sace wasu mutane 8 a garin Kwassam da ke ƙaramar hukumar Kauru a jihar Kaduna.

‘Yan bindigar sun kashe wani likita tare da yin garkuwa da wasu mutane 8 a garin Kwassam da ke ƙaramar hukumar Kauru a jihar Kaduna.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, ɗan majalisar tarayya na Mazabar Kauru, Hon. Zakari Ahmad Chawai, ya ce ana yawan samun hare-haren akai akai a mazaɓun Kwassam da Dawaki dake ƙaramar hukumar ta Kauru.

“Kwanaki huɗu da suka wuce ’yan bindigar sun kai hari a wata unguwa dake cikin mazaɓar Dawaki inda suka sace wasu mazauna yankin, kuma jiya sun sake kai hari a unguwar Kwassam,” in ji shi.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga a Binuwai sun ƙona gidaje 23

Yace, masu garkuwa da mutanen sun kashe mutun ɗaya, sun sace mutane 8 kuma sun tafi da wasu kayayyakin mutane da ba’a tantance adadinsu ba.

Hon. Chawai ya yi ƙira ga jami’an tsaro da su ƙara ƙaimi wajen magance hare-haren dake yawan faruwa a yankunan Kwassam da Dawaki.

Rahotanni sun nuna cewa mazauna yankin suna ci gaba da gudanar da ayyukansu na yau da kullum kamar yadda suka saba bayan lafawar abin.

Sai dai har yanzu babu wani bayani daga masu garkuwar kan batun kuɗin fansa, kamar yadda wani mazaunin Kwassam ya shaidawa manema labarai.

Continue Reading

You May Like