No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wata ‘yar sanda mai suna Angela Adams a ranar Talata ta roƙi wata kotun gargajiya da ke zamanta a Jikwoyi, babban birnin tarayya Abuja, da ta raba auren da ke tsakaninta da mijinta, Titus, kan rikicin cikin gida.

Matar ta faɗi haka ne a cikin ƙarar da ta shigar a gaban kotun game da mijinta.

“Mijina yakan yi min duka a duk lokacin da muka samu ‘yar rashin fahimta. Yakan yi min duka kamar ƙaramar yarinya.

“Koda yaushe idona ya ke nema idan yana duka na. Ko rannan ma da ya yi min duka, sai da ya kawo min naushi a fuskata, na yi sa’a na kare da hannuna amma duk da haka sai da naushin ya ji min rauni a hannu na,” in ji ta, lokacin da ta ke kuka.

KU KUMA KARANTA: Kotu ta raba auren wata 10 ta hanyar “Khul’i”

Ta ce mijin nata ya karɓi rancen kuɗi naira dubu 750,000 da sunan ta a wani banki.

“Lokacin da na tambaye shi me zai yi da kuɗin, sai ya gaya min cewa ya sayi katako ne da kwanon rufi ɗaki da kuɗin, amma daga baya na ji cewa ashe wani gida ya kama haya ya gyara shi ya saka wata mace a ciki.”

Yaudara ta ya yi na aure shi, ban san ma ashe ya na da ‘ya’ya biyu ba, kuma kwanan nan ya yi wa wata ciki.”

“Ina roƙon wannan kotu mai daraja da ta ba ni riƙon ɗan ɗaya tilo na wannan aure tare da raba auren kafin mijina ya kashe ni kuma ba za a samu wanda zai kula da yaro na ba”.

Wanda ake ƙara,Titus wanda shi ma ɗan sanda ne, bai halarci zaman kotun ba.

Sai dai mai shari’a Thelma Baba, ta bayar da umarnin a kai ƙarar wanda ake ƙara ta hannun lauyansa, sannan ta ɗage ci gaba da sauraron ƙarar har zuwa ranar 24 ga watan Oktoba, domin jin ta bakin wanda ake ƙara da kuma kare kansa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...