Connect with us

Labarai

Wata uku gwamnatin da na gada ba ta biya albashi ba a Zamfara – Gwamna Dauda

Published

on

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare, ya ce yana tafiyar da jihar ne a kan bashi tun bayan hawansa mulki a ranar 29 ga watan Mayu.

Ya kuma ce gwamnati ta ka sa biyan albashin ma’aikata da alawus-alawus, ciki har da hukumomin tsaro a jihar.

Gwamna Lawal, wanda ya bayyana haka a wata hira da ya yi da BBC Hausa a ranar Litinin, ya ce gwamnatin da ta shuɗe ta bar ƙa sa da naira miliyan huɗu ne kawai kacal a asusun jihar.

A cewarsa, manyan ɗaliban makarantun jihar ba su rubuta jarabawar kammala sakandire ta Afirka ta Yamma, (WAEC), da hukumar jarrabawar NECO ba, saboda rashin kuɗi.

KU KUMA KARANTA: Ban mallaki kadarorin naira tiriliyan 9 ba – Gwamnan Zamfara

“Na kasance ina tafiyar da al’amuran jihar a kan bashi tun lokacin da na hau kujerar gwamnan Zamfara.

Na samu asusun baitul malin jihar ba kuɗi. Na ga asusu ɗaya da kusan Naira miliyan 3 zuwa 4 a ciki,” inji shi.

“Kusan watanni uku ke nan, kuma har yanzu ba mu biya albashin ma’aikata ba.

Idan aka dubi dukkan hukumomin gwamnati, wutar lantarkin da ake amfani da su a gine-ginen ya katse saboda basussukan da ake bi na miliyoyin daloli.

“Hukumomin tsaro, watanni uku kenan ba a biya su alawus ɗin da ake ba su na ayyukan yau da kullum ba.

Yanzu haka ɗaliban manyan makarantun sakandire ba su rubuta jarabawar WAEC da NECO ba saboda gwamnati na bin sama da naira biliyan ɗaya.”

Yayin da yake watsi da iƙirarin da tsohon gwamnan ya yi na cewa ya bar wa sabon gwamnan Naira biliyan 20, gwamna Lawal ya ƙalubalanci shi da ya gabatar da shaidun da ke nuna adadin kuɗin a bainar jama’a.

Ya ce, “Lokacin da na ji haka, sai na ce su zo su nuna mini asusun, su bayyana shi tare da shaidar asusun da aka ajiye irin waɗannan maƙudan kuɗaɗe,” inji shi.

“Idan ina da wannan adadin kuɗaɗen da gwamnatin da ta shuɗe ke iƙirarin sun bar jihar, zan biya dukkan ma’aikata albashin su, in kuma samar da isassun kuɗaɗen ga jami’an tsaro domin kare jihar.

“Batun ruwa, kusan watanni huɗu kenan babu ruwa a Gusau.

Dole ne in yi aro don siyan sinadarai na ruwan. “Na kuma roƙi wasu Indiyawan da suka baiwa jihar wasu injunan samar da ruwa.

Idan jihar za ta sayi waɗannan injunan, za ta kashe sama da Naira miliyan 200.

“Ba zan iya cewa na magance matsalar ruwa ta Zamfara ta dindindin ba, amma zan yi iya ƙoƙarina don ganin an magance matsalar,” in ji Dauda.

Gwamnan ya ce zai tabbatar da an biya ma’aikatan jihar albashinsu kafin gudanar da bukukuwan Sallah. “Ina so in tabbatar wa ma’aikatan gwamnati a Zamfara cewa za mu yi iya ƙoƙarinmu don ganin an biya dukkan albashin ma’aikata kafin Sallah,” in ji shi.

“Zan yi duk abin da ya kamata don biyan albashin ma’aikata. Ina yin duk abin da ya dace don nemo tallafi don biyan albashin da ake binsa.

“Ya danganta da adadin lamunin da zan iya samu. Idan har abin da jihar za ta iya biya shi ne albashin wata ɗaya, zan yi iya ƙoƙarina wajen biya shi domin haƙƙinmu ne mu tabbatar mun gudanar da aikin da ya rataya a wuyanmu na biyan ma’aikata abin da suka yi aiki a kai.”

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Kotu ta dawo da mataimakin Matawalle da aka tsige | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like