No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Ribas sun cafke wata uwar ‘ya’ya biyu da ta watsa wa mijinta Acid a fuska a kan rabon Naira 15,000 da aka biya kowane iyali a unguwar Nchia da ke ƙaramar hukumar Eleme.

Mummunan lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar Asabar, 14 ga watan Oktoba.

Rahotanni sun bayyana cewa, matar ta samu rashin jituwa da mijin ta wanda ta yi zargin ya ƙwace kason Naira 15,000 da aka baiwa iyalan da kamfanoni na ƙasa da ƙasa da ke yankin suka ba al’ummar .

Ta ce mijin ya ƙi biyan ta kasonta na ‘ya’ya biyu daga cikin kuɗin.

A fusace matar ta zuba wa mijin nata acid sannan ta ƙwace masa katin ATM ɗin sa ta yi yunƙurin tserewa.

KU KUMA KARANTA: Uwargida ta zuba wa maigida tafasasshen man gyaɗa yana cikin barci, ta kwaɗa masa guduma ta gudu

Sakamakon haka mijin ya yi kururuwa wanda ya ja hankalin ‘yan banga. Ganin ‘yan banga sun biyo ta, sai ta gudu ta koma gida ta boye a cikin silin.

Daga bisani ‘yan banga sun sauƙo da ita daga silin na gidan, suka miƙa ta ga ‘yan sandan garin Eleme dake ƙaramar hukumar Eleme don ci gaba da bincike, yayin da aka garzaya da mijin zuwa wani asibiti da ba a bayyana ba domin neman kulawar gaggawa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...