Connect with us

Labarai

Wasu ‘yan bindiga sun kashe ma’aikacin INEC, sun sace matarsa a Ebonyi

Published

on

Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton masu garkuwa da mutane ne sun kashe ma’aikacin hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) a jihar Ebonyi.

Wanda aka kashe, Emnanuel Igwe, mataimakin jami’in zaɓe, AEO, an kashe shi ne a hanyar Ishiagu na hanyar Ishiagu zuwa Mpu a yammacin Lahadin da ta gabata yayin da yake dawowa daga jihar Anambra.

An kuma bayyana cewa ‘yan bindigar sun sace matar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kashe basaraken gargajiya da ‘ya’yansa huɗu, sun sace shanu 100 a Kaduna

Jami’in hulɗa da jama’a na ‘yan sandan, SP Onome Onovwakpoyeya, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Litinin a Abakaliki, ya ce an aike da tawagar ƙwararrun ‘yan sanda domin farauto masu laifin.

Ta ce: “Eh, an kai harin inda aka harbe mutum ɗaya a ka ta fuskar gilashin, kuma ba a ɗauke komai daga cikin motar, kuma ɗayan da aka kashen wani manomi ne da ke aiki a gonarsa wanda suka yanke maƙogwaro.

Wasu ’yan asalin yankin Ishiagu da ke ƙaramar hukumar Ivo ta Jihar Ebonyi a Abakaliki, waɗanda suka mayar da martani kan lamarin a hirarsu da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, sun yi ƙira ga ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro da su daƙile matsalar tsaro da ke kunno kai a kan hanyar Ishiagu zuwa Mpu.

Shugaban matasan Ohanaeze Ndigbo, Cif Damian Okoafor, wanda ya tabbatar da kisan mahaifinsa ga manema labarai a Abakaliki a ranar Litinin, ya ce wasu da ake zargin makiyaya ne suka mamaye al’umma a ranar lahadin da ta gabata kuma suka aikata wannan mummunan aiki.

“Waɗanda ake zargin makiyaya ne suka sake kai hari a unguwar Ishiagu, suka kashe mahaifina, wani mutum ɗaya sannan suka sace daya,” inji shi.

Nicholas Onu, ma’aikacin hukumar zaɓe ta INEC a hedikwatar Abakaliki, ya bayyana cewa wanda aka kashe abokin aikinsu ne, yana mai cewa hasarar ta yi yawa.

Ya yi ƙira da a gaggauta tura tawagar jami’an tsaro na haɗin gwiwa na ‘yan sanda da sojoji domin daƙile sace-sacen mutane da fashi da makami da sauran miyagun laifuka a kan hanyar.

“Masu garkuwa da mutane da ake zargin makiyaya ne sun harbe Mista Emmanuel Igwe har lahira a lokacin da suka yi awon gaba da matarsa.

“Bayanin bayanan da ‘yan uwa suka samu sun nuna cewa an kwashe gawar an ajiye ta a ɗakin ajiye gawa da ke Abakaliki yayin da waɗanda ake zargin ke neman kuɗin fansa naira miliyan 10,” in ji Mista Onu.

Dokta Innocent Mbazu, malami a Kwalejin Ilimi ta Jihar Ebonyi, Ikwo, wanda ke zaune a Abakaliki, ya buƙaci ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro su shiga tsakani cikin gaggawa, yana mai bayyana lamarin a matsayin ‘abin takaici.

“An yi garkuwa da wani direban mota tare da kashe wani ɗan uwanmu a gonarsa a ranar Lahadi a kan titin Ishiagu na hanyar Ishiagu zuwa Mpu.

“Duk wanda ke da niyyar amfani da hanyar ya kamata ya yi kasuwanci da hankali ko kuma ya guje wa hanyar a yanzu idan zai yiwu.

Da alama masu garkuwa da mutane da ke aiki a kan babbar hanyar Amaeze-Awgu sun koma ta Mpu.

“An ce mutanen Ngwogwo a Ishiagu suna zanga-zanga a halin yanzu. Allah ya taimake mu!!,” Mbazu ya koka.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Su waye suka sace fitilun titin tashan jirgin sama na Legas? | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Su waye suka sace fitilun titin tashan jirgin sama na Legas? - LEGEND FM DAURA

  3. Pingback: ‘Yan sanda sun tabbatar da sakin Rabaran Father da aka sace a Ebonyi | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Published

on

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

A ƙoƙarinsa na kauce wa rikicin manoma da makiyaya da ke yawan faruwa a lokacin damuna, Shugaban Karamar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, Dakta Ahmed Wali Doho, ya kafa kwamitin tsaro da sanya ido kan ɓangarorin.

Da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke garin Malam Sidi, shugaban karamar hukumar, ya bukaci manoma da su guji noma burtalolin shanu, wanda hakan ke haifar da rikici tsakaninsu da makiyaya, da ke haifar da asarar rayuka.

Su ma makiyayan ya gargade su da cewa su guji shiga gonakin manoma, saboda hakan ne ke jawo rikici idan suka cinye musu amfanin gona.

A cewarsa, lokacin girbi me aka fi samun rikicin manoma da makiyayan, saboda haka kwamitin zai ci gaba da sa ido daga yanzu har zuwa lokacin girbin don ganin ba a samu rikici ba.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Yusuf ya amince da sayen taki na naira biliyan 5 don manoman Kano

Ya ƙara da cewa, kusancin garin Kwami da rafi ya sa ya zama wuri mai kyau don noman rani.

Don haka ya ja hankalin manoman yankin da su yi amfani da wannan damar wajen bunkasa tattalin arzikinsu.

Ya jaddada cewa noman rani na da matukar muhimmanci wajen magance matsalar karancin abinci a Najeriya.

Hakan ne ya sa suka haɗa kan matasan yankin don su fara noman rogo da zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin abinci da rage wa manoma tsadar takin zamani.

Continue Reading

Labarai

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Published

on

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da ɓata-garin cikin

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da bata-gari a cikinsu.

Kwamishin ’yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya sanar da shirin bayan an kama wasu ’yan banga uku da aikata manyan laifuka.

Ya jaddada muhimmancin sake duba ayyukan ’yan banga a jihar, duk da  muhimmiyar rawar da suke takawa wajen taimaka wa jami’an tsaro a yaki da miyagun laifuka.

Ya ce yin gyaran da kuma tantancewa ya zama dole sakamakon ƙorafe-ƙorafen neman yin hakan daga jama’a.

Ya bayyana cewa jama’a sun yi ƙiran ne bayan kama wasu ’yan banga uku da laifin hada baki wajen shiga gida, sata, ƙwace da kuma sayar da kayan sata a Damaturu.

Wata sanarwa da DSP Dungus Abdul Karim, kakakin rundunar, ya fitar, ta ce wasu daga cikin ’yan banga sun kai korafi bayan faruwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara

“A ranar 27 ga watan Yuni, 2024, rundunar ta amsa kiran wani mai shago a Damaturu, wanda ya dauki ’yan banga aikin gadi, amma suka kwashe kayan shagon na makudan kudade ba tare da bayani ba.

“Bincike ya kai ga kama wasu mutane biyu da kayan sata da ake zargin sun saya ne daga wani dan banga wanda nan take aka kama shi.

“Ana shawarta jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen daukar masu gadi, sannan su kai rahoton ’yan banga da aka ga suna aikata laifi a bakin aikinsu.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, rundunar tana ɓullo da tsare-tsare don daukar bayanan ’yan banga domin sa ido kan ayyukansu.

Ta ci gaba da cewa ofisoshin ’yan sanda na yankuna da ke jihar za su jagoranci wannan aikin tantancewan domin kawar da baragurbi a cikin ’yan banga.

“Don  haka ake ƙira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda wajen jainrahoton ayyukan jami’an tsaron da ba su dace ba a hedkwatar jihar ta lamba 07068858500, ko kuma a gabatar da wasikar korafin ga kwamishinan ’yan sanda  ta hanyar kakakin rundunar,” in ji sanarwar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like