No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton masu garkuwa da mutane ne sun kashe ma’aikacin hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) a jihar Ebonyi.

Wanda aka kashe, Emnanuel Igwe, mataimakin jami’in zaɓe, AEO, an kashe shi ne a hanyar Ishiagu na hanyar Ishiagu zuwa Mpu a yammacin Lahadin da ta gabata yayin da yake dawowa daga jihar Anambra.

An kuma bayyana cewa ‘yan bindigar sun sace matar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kashe basaraken gargajiya da ‘ya’yansa huɗu, sun sace shanu 100 a Kaduna

Jami’in hulɗa da jama’a na ‘yan sandan, SP Onome Onovwakpoyeya, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Litinin a Abakaliki, ya ce an aike da tawagar ƙwararrun ‘yan sanda domin farauto masu laifin.

Ta ce: “Eh, an kai harin inda aka harbe mutum ɗaya a ka ta fuskar gilashin, kuma ba a ɗauke komai daga cikin motar, kuma ɗayan da aka kashen wani manomi ne da ke aiki a gonarsa wanda suka yanke maƙogwaro.

Wasu ’yan asalin yankin Ishiagu da ke ƙaramar hukumar Ivo ta Jihar Ebonyi a Abakaliki, waɗanda suka mayar da martani kan lamarin a hirarsu da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, sun yi ƙira ga ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro da su daƙile matsalar tsaro da ke kunno kai a kan hanyar Ishiagu zuwa Mpu.

Shugaban matasan Ohanaeze Ndigbo, Cif Damian Okoafor, wanda ya tabbatar da kisan mahaifinsa ga manema labarai a Abakaliki a ranar Litinin, ya ce wasu da ake zargin makiyaya ne suka mamaye al’umma a ranar lahadin da ta gabata kuma suka aikata wannan mummunan aiki.

“Waɗanda ake zargin makiyaya ne suka sake kai hari a unguwar Ishiagu, suka kashe mahaifina, wani mutum ɗaya sannan suka sace daya,” inji shi.

Nicholas Onu, ma’aikacin hukumar zaɓe ta INEC a hedikwatar Abakaliki, ya bayyana cewa wanda aka kashe abokin aikinsu ne, yana mai cewa hasarar ta yi yawa.

Ya yi ƙira da a gaggauta tura tawagar jami’an tsaro na haɗin gwiwa na ‘yan sanda da sojoji domin daƙile sace-sacen mutane da fashi da makami da sauran miyagun laifuka a kan hanyar.

“Masu garkuwa da mutane da ake zargin makiyaya ne sun harbe Mista Emmanuel Igwe har lahira a lokacin da suka yi awon gaba da matarsa.

“Bayanin bayanan da ‘yan uwa suka samu sun nuna cewa an kwashe gawar an ajiye ta a ɗakin ajiye gawa da ke Abakaliki yayin da waɗanda ake zargin ke neman kuɗin fansa naira miliyan 10,” in ji Mista Onu.

Dokta Innocent Mbazu, malami a Kwalejin Ilimi ta Jihar Ebonyi, Ikwo, wanda ke zaune a Abakaliki, ya buƙaci ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro su shiga tsakani cikin gaggawa, yana mai bayyana lamarin a matsayin ‘abin takaici.

“An yi garkuwa da wani direban mota tare da kashe wani ɗan uwanmu a gonarsa a ranar Lahadi a kan titin Ishiagu na hanyar Ishiagu zuwa Mpu.

“Duk wanda ke da niyyar amfani da hanyar ya kamata ya yi kasuwanci da hankali ko kuma ya guje wa hanyar a yanzu idan zai yiwu.

Da alama masu garkuwa da mutane da ke aiki a kan babbar hanyar Amaeze-Awgu sun koma ta Mpu.

“An ce mutanen Ngwogwo a Ishiagu suna zanga-zanga a halin yanzu. Allah ya taimake mu!!,” Mbazu ya koka.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

3 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...