No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun hallaka fararen hula 8

Aƙalla mutane 8 sun mutu a arewacin Togo a wani saban harin da ‘yan bindiga suka kai a arewacin ƙasar.

Majiyoyi daga wasu mazauna ƙauyukan sun shaida cewa  ‘yan bindigar sun zo ne a cikin daren juma’a wayewa safiyar asabar inda bayan sunyi kutse a wani gida  da aka tsugunar da ‘yan gudun hijira  suka yi wa mai gidan da sauran mutane 7 kisan gilla.

Majiya ta ƙara da cewa a wanan karon  ‘yan bindigar sun hari ƙauyen Malgabangou  ne an kuma kiyasta aƙalla mutane 8 sun mutu.

Wanan shi ne karo na biyu a cikin makwani biyu da yankin ya fuskanci harin ‘yan bindiga.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga a Zamfara sun harbi babban kwamandan dakarun sa kai

Kawo yanzu dai babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin kai harin, sai dai a baya ƙungiyar mayaƙa masu iƙirarin Jihadi ta JNIM ta sha kai hare hare a baya a wanan yankin.

Tun daga shekara 2021, ƙauyukan dake yammacin gunduma Kpendjal a ƙasar ta Togo ke fuskanta hare haren ‘yan bindiga masu ɗauke da makamai.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...