Connect with us

Labarai

A sama mana sana’ar yi – Tubabbun ‘yan Boko Haram

Published

on

Tubabbun ‘yan ta’addan Boko Haram sun yi ƙira ga gwamnati da ta samar musu da hanyoyin rayuwa yayin da suke sake tsugunar da su cikin al’ummomin da aka yi musu gyara.

A lokacin da take zantawa da ‘News Point Nigeria’ kaɗai a cibiyar farfaɗo da Bulumkutu da ke Maiduguri inda ministar harkokin jin ƙai da yaƙi da fatara, Betta Edu ta raba musu kayan abinci da kuma wasu ‘yan matan Chiɓok da aka ceto, tsoffin ‘yan ta’addan sun bayyana damuwarsu kan halin da suke ciki a halin yanzu, inda suka ƙara da cewa wasu daga cikinsu suna tunanin komawa daji.

“Har yanzu ina zaune a sansanin duk da cewa hukumomi sun sako ni amma ba ni da inda zan je, yawancin mu ba su da aiki har wasu na tunanin komawa daji.

“Ni mai gyaran walda ne kuma mai gyaran bindigu a Sambisa, lokacin da nake miƙa wuya na kawo bindigu biyar a matsayin gudunmawata ga gwamnatin Najeriya,” in ji ɗaya daga cikin tubabbun mayaƙan Boko Haram, Ali Kaka.

Wani tubabbun mayaƙan Boko Haram, Suleiman Abubakar, ya ce, “Ni ɗaya ne daga cikin waɗanda suka miƙa makamansu kuma na yi hakan ne saboda na gaji da kashe-kashe da sata kuma ina buƙatar fara sabuwar rayuwa.

KU KUMA KARANTA: Boko Haram a Borno sun yi garkuwa da mata bakwai, sun kashe biyar

“Mun ɗauki makami ne saboda rashin aikin yi ko kuma tabbatacciyar hanyar rayuwa don haka zan roƙi gwamnati da ta samar mana da hanyar rayuwa ta yadda wasun mu da suka miƙa wuya da gaske ba za su sake gwadawa ba.”

Yayin da yake mayar da martani ga roƙon nasu, Ministan ya ce Gwamnatin Tarayya tana bakin ƙoƙarinta wajen ganin ta rage raɗaɗin talauci a tsakanin talakawa a cikin al’umma ta fara samar da tallafi da rance mai sauƙi wanda nan ba da daɗewa ba za a fara.

Duk waɗanda suka tuba da ceto ‘yan matan Chiɓok da sauran su sun taru a yawansu domin tarbar ministar.

Cibiyar farfaɗo da Bulumkutu ita ce ake ajiye waɗanda aka ceto da suka haɗa da ‘yan matan makarantar Chiɓok da tubabbun ‘yan tada ƙayar baya domin sa ido da tantance su kafin a sake shigar da su cikin al’umma.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like