Connect with us

Labarai

Wasu fitinannun ɓeraye sun tilasta wa manoma kwana a gona a Kano

Published

on

Wasu murguza-murguzan ɓeraye sun tilasta wa manoma kwana a gonakin su domin yin gadi, sakamakon ɓarna da su ke yi musu ta amfanin gona a yankin ƙananan hukumomin Kura, Bunkure da Garin Mallam a jihar Kano.

Manoman dai sun bayyana cewa ɓerayen sun zame musu annoba, musamman ma ganin cewa duk irin maganin kashe bera da aka saka musu, amma sai su ƙi ci, lamarin da ya sanya su ka ɗauki matakin yin fito-na-fito da su.

Sun kuma baiyana cewa idan suka bar gona to sai dai a yiwa manomi jaje, inda su ka ce ɓerayen ba sa tsoron mage ballantana muzuru.

Mallam Ahmed sani kura wani malamin gona ne ya yankin Dan Galawa dake ƙaramar hukumar Kura daga ƙungiyar masu anfani da ruwan noman rani, ya yi ƙira ga gwamnati da ta kawo musu ɗauki.

Ya kuma yi ƙira ga masana da su bada gudummawar hanyar da za a samu nasarar kashe ɓerayen ta hanyar zuba musu guba a abinci.

KU KUMA KARANTA: Manoma sun koka kan yadda makiyaya ke cinye musu gonaki a Gombe

A nashi ɓangaren, Alhaji Sani Danladi Yadakwari, shugaban ƙungiyar masu noman tumatur ta ƙasa reshan jihar Kano ya ce wannan ɓeraye sun daɗe suna uzzirawa manoma kuma suna zuwa ne lokacin sanyi.

Ya koka da cewa duk irin girman gonar manomi idan ba a yi wasa ba sai sun cinye ta.

“Wato wasu irin murguza-murguzan ɓeraye ne masu laifin basira domin duk irin maganin ɓera da ka saka musu a abinci banza su ci ba. Idan ka saka magani a abinci ka ajiye wani abincin maras magani, to maras maganin za su ci.

“Duk yawan shuka da aka yi sai sun cinye ta. Hakan ne ya sanya dole manoma da yawa su ka koma kwana a gonakin su domin gadin ganin gonar su da kuma kashe ɓerayen.

“Muna ƙira ga gwamnati da ta kawo mana ɗauki sannan muna ƙira ga masana ilimin dabbobi dan su tallafa mana da hanyoyi ko nau’in maganin da za a riƙa saka musu suna mutuwa,” in ji Yadakwari.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like