Connect with us

Labarai

Wasu ɓarayi sun girbe gonakin shinkafa a Taraba

Published

on

Gungun wasu ɓarayi sun fatattaki masu gadin wasu manyan gonakin shinkafa, suka girbe ta suka yi awon gaba ita a jihar Taraba.

A cikin dare ne barayin suka shiga yankin Shimo da ake karamar hukumar Lau ta jihar, suka kori masu gadin suka girbe shinkafar suka tafi da ita.

Daya daga cikin masu gonakin, Abubakar Adamu, ya ce mai gadin da ya dauka aiki ya shaida masa cewa barayin sun zo ne da yawa dauke da muggan makamai. Abin da ya janyo dole suka ranta a ta kare domin tsira da rayukansu.

Ya ce, barayin sun iso gonakin ne da misalin karfe 12:30 na dare suka fara yankar shinkafar har  zuwa asuba.

KU KUMA KARANTA: An tsare ɓarayi 2 kan satar buhun zoɓo 10 a Jigawa

Abubakar ya bayyana cewa yana fatan girbar buhunan shinkafa sama da 25 amma bayan satar iya buhu takwas kacal ya girba.

“Mai gadina ya shaida min cewa barayin sun fito ne daga kauyukan da ke makwabtaka da gonata, wasunsu kuma leburorin da ke aiki a gonakin namu ne.”

Malam Ibrahim Saidu wanda shi ma aka shiga gonarsa, ya shaida mana cewa, wannan babbar sata ce da aka shirya.

Domin a cewarsa, ɓarayin da kafa suka zo wasu kuma a kan babura.

Ibrahim, wanda ya zargi mazauna kauyukan da ke kewaye da gonakinsu ne da yin satar, ya ce ya yi asarar buhunan shinkafa sama da talatin.

A cewarsa, a halin yanzu da shinkafa ke tsada, asarar da ya yi za ta kai kimanin Naira miliyan daya da dubu dari uku.

“Ba mu kama kowa ba, amma a fayyace yake cewa wadanda suka aikata wannan aika-aika ’yan yankin ne kuma wannan wani sako ne mai tsoratawa, musamman ganin yadda yawancin wadanda ke noma a yankin sun fito ne daga wajen jihar Taraba.

Bincike ya nuna cewa an dade ana satar amfanin gona a yankin noman rani na Shimo a jihar Tarba, abin da yasa yankin ya zamo abin tsoro.

Duk kokarinmu na jin ta bakin kwamishinan ’yan sandan jihar Taraba David lloyanomon kan abin da suke shirin yi abin ya ci tura.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like