Connect with us

Labarai

Wani soja a Borno ya kashe direban kayan agaji kan na-goro

Published

on

Wani soja ya kashe direban motar kayan agaji da saboda ƙin ba shi na-goro a hanyar Dikwa zuwa Gamboru da ke Jihar Borno.

A safiyar Alhamis ce Sakataren Ƙungiyar Ma’aikatan Sufurin (NURTW) Ahmed Musa ya sanar cewa direban da sojan ya kashe na ɗauke da kayan agaji ne zuwa N’djamena na Jamhuriyar Chadi.

Musa ya tabbatar cewa direban ya samu izini daga hedkwatar sojoji da kwamandan rundunar Operation Haɗin Kai na Arewa maso Gabas, amma duk da haka sojan da ke wani shingen binciken ababen hawa ya nemi ya ba shi kuɗi.

“Amma ya bayyana wa sojan cewa kayayyakin jinkai ne a cikin motar kuma kwamandan rundunar ya sahale musu, inda  ya ba da takardar izinin.

KU KUMA KARANTA: Budurwa ta yi amfani da bindigar ɗan sanda ta harbe shi har lahira

Duk da haka, sojan ya yi watsi da takardun ya lakaɗa wa direban da yaronsa duka da kotar bindiga, har sai da direban ya suma, daga baya ya ce ga garinku nan.

“Haka muke rasa direbobi a sakamakon zaluncin da sojoji a hanyar Gambarou, shi ya sa muka yanke shawarar rufe hanyar har sai an ɗauki mataki,” inji shi.

Muƙaddashin Daraktan Yaɗa Labaran Rundunar Soji ta 7 da ke Maiduguri, Laftanar-Kanar Ajemusu Y Jingina ya tabbatar da labarin da kuma tsare sojan da samun ya kashe direban motar.

“Rundunar runduna ta 7 ta Najeriya ta samu koke daga ƙungiyar NURTW reshen Jihar Borno cewa wani soja ya kashe wani direban babbar mota mai suna Mohammed Bello a wani shingen bincike a kan hanyar Dikwa-Gamboru a ranar 26 ga watan Disamba, 2023.

“Samun ƙorafin ke da wuya rundunarmu ta hanzarta ɗaukar mataki, kuma ƙoƙarin ganin iyalan mamacin sun samu adalci, an kama sojan da ake zargi, kuma an fara bincike kan lamarin.”

Ya bayyana cewa rundunar da ƙungiyar NURTW sun ƙulla yarjejeniya domin ganin an shawo kan lamarin cikin lumana, da kuma tabbatar da adalci ga iyalan mamacin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like