Connect with us

Labarai

Wani saurayi ya chaka wa liman wuƙa saboda ya hana shi shan tabar wiwi a kusa da Masallaci

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta cafke wani kasurgumin ɗan daba mai suna Yusuf Haruna AKA Lagwatsani mai shekaru 18 bisa laifin kashe wani fitaccen limami mai suna Malam Sani Mohammed Shuaibu.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Abdullahi Kiyawa Haruna, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Laraba, 3 ga watan Janairu, 2024, ya ce Haruna, na karamar hukumar Dala ta jihar, ya daɓa wa malamin wuƙa har lahira bayan marigayin ya yi ƙoƙarin hana shi da ’yan ƙungiyarsa shan tabar wiwi a kusa da harabar Masallacin.

 “A ranar 31/12/2023 da misalin karfe 1930 ne aka samu rahoto daga wani Musa Yunusa ‘m’ na Jakara Quarters Kano cewa a ranar da misalin ƙarfe 1900, Yusuf Haruna ya kai hari tare da daɓa wa wani Malam Sani Mohammed Shuaibu mai shekaru 45 wuƙa mai kaifi a bayansa yayin da yake alwala, kawai saboda wanda abin ya shafa ya gargaɗe shi da ‘yan ƙungiyarsa da su daina shan tabar wiwi a kusa da harabar Masallacin,” in ji sanarwar.

KU KUMA KARANTA: An yi wa Alkali dukan kawo wuka a Gombe

“Saboda haka, wanda abin ya shafa ya samu rauni sosai, aka garzaya da shi asibitin ƙwararru na Murtala Muhammed, kuma likita ya tabbatar da mutuwarsa.

“Lamarin ya girgiza al’umma, kuma jami’an mu sun yi bakin ƙoƙarinsu wajen zaƙulo maharin tare da kama shi.  Wannan kamun ya shaida mana jajircewarmu na kare martabar rayuwa da kuma tabbatar da adalci ga waɗanda irin waɗannan munanan ayyuka suka shafa.”

PPRO ya ƙara da cewa kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Mohammed Usaini Gumel, ya baiwa jama’a tabbacin hukumar ta ɗau alwashin gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

“Bugu da ƙari, za mu yi aiki tuƙuru don tattara ƙwararan hujjoji don tabbatar da nasarar gurfanar da mutanen da aka kama.”

“Manufarmu ba wai kawai mu gurfanar da waɗanda suka aikata laifin a gaban ƙuliya ba ne, har ma da zama kange ga wasu da za su yi tunanin irin wannan aika-aikar.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like