Wani mutum a Legas ya rasu sakamakon azumin kwana 19

0
66
Wani mutum a Legas ya rasu sakamakon azumin kwana 19

Wani mutum a Legas ya rasu sakamakon azumin kwana 19

Rundunar ’yan sandan jihar Legas, ta tabbatar da rasuwar wani mutum mai shekara 58, sakamakon shafe kwanaki 19 yana azumin ba tare da ya sha ruwa ba.

Kakakin rundunar ’yan sandan, SP Benjamin Hundeyin ne, ya bayyana hakan a ranar Talata.

Ya ce lamarin ya faru ne a yankin Alagbado na jihar a ranar Litinin da misalin ƙarfe 6 na safe.

Ya ce ɗan uwan mamaci ne, ya kai rahoto faruwar lamarin ofishin ‘yan sanda na Alagbado a ranar Litinin cewa ɗan uwansa ya rasu sakamakon shafe kwanaki 19 yana azumi.

KU KUMA KARANTA: Tsohon shugaban hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka, Issa Hayatou, ya rasu

Hundeyin ya ce, “Babu wani abu da aka zargi ya faru da shi, ‘yan uwansa sun buƙaci a kai gawar don birne ta.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here