Wani matashi ya kashe mahaifinsa, ya binne shi a gidansu

0
55
Wani matashi ya kashe mahaifinsa, ya binne shi a gidansu

Wani matashi ya kashe mahaifinsa, ya binne shi a gidansu

Rundunar ’yan sandan jihar Neja, ta kama wani matashi mai shekara 29 mai suna Mizanmil Abubakar da laifin kashe mahaifinsa Abubakar Adawa mai shekara 65 a duniya.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Waisu Abiodun ne, ya bayyana hakan a Minna a ranar Talata, inda ya ce an kai rahoton faruwar lamarin sashen ‘yan sanda na Kpakungu.

Ya ce, “A ranar Talata da misalin ƙarfe 10 na safe ne aka samu labari a sashen Kpakungu cewa a ranar Litinin wani Abubakar Adawa ya ɓace a unguwar Barkin-Sale a Minna.

Abiodun ya ce jami’an ’yan sandan da ke aiki a sashen ƙarƙashin jagorancin jami’in ‘yan sanda na yankin sun ziyarci gidan da wani Mizanmil Abubakar mai shekara 29 da kuma Aisha Abubakar, uwa da ɗanta ke ciki domin yi musu tambayoyi.

Ya ce, “An yi bincike sosai a gidan baki ɗaya, kuma abin mamaki, an gano gawar wanda ya ɓace a cikin wani rami mara zurfi a gidan.”

KU KUMA KARANTA: Mayaƙan ‘Boko Haram’ a Borno sun kashe ɗan sanda da ƙona motocin sintiri

Abiodun, ya ce matashin ya amsa laifin kashe mahaifinsa ne sakamakon ya tsane shi.

Kakakin ya ce wanda ake zargin ya amsa cewa ya yi amfani da fartanya ne wajen kashe mahaifin nasa, sannan ya birne shi a wani rami.

Ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin kafin miƙa wanda ake zargin a kotu.