No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani matashi a Kano ya kai wa ‘yan sanda kuɗin da ya tsinta

Daga Idris Umar, Zariya

Wani direba mai shekaru 36, mai suna Safiyanu Mohammed ya miƙawa ‘yan sandan jihar Kano wata jaka ɗauke da maƙudan kuɗaɗe da ya tsinta.

Kakakin rundunar ‘yan sandar jihar Kano, SP Abdallahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi.

A cewar sa direban wanda mazaunin unguwar Rangaza kwatas ne a ƙaramar hukumar Ungogo, ya tsinci jakar ne a ranar Juma’a 9 ga watan Agusta, 2024 a hanyar Hadejia kusa da mahaɗar Dakata.

KU KUMA KARANTA: An karrama ɗan agajin da ya tsinci miliyan 100

A maimakon ya tafi da kuɗin, Mohammed ya zaɓi ya mika wa hukumar ƴansanda jakar da domin gano mai jakar don bashi abarsa.

Rundunar ‘yan sandar jihar ta Kano ta yi ƙira ga jama’a da su taimaka musu da cikakkun bayanai da zai sa a gano mai jakar don bashi jakarsa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...