Wani ɗalibin Islamiyya ya kashe kansa wai saboda Allah bai amsa addu’arsa ba

0
151

Wani ɗalibi ɗan shekara 22 a makarantar Sheikh Kamaldeen Arabic da ke Ilorin a jihar Kwara ya kashe kansa.

Ɗalibin mai suna Alfa Musa, an same shi ne a rataye a ɗakinsa da ke harabar Dagbenu a unguwar Ogidi a Ilorin a ranar Alhamis 7 ga watan Disamba, 2023.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Ejire Adetoun Adeyemi, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya bayyana cewa an fara bincike kan lamarin.

PPRO ya ce marigayin ya bar wa iyayensa takardar kashe kansa watau “suicide note” .

KU KUMA KARANTA: Ɗan kasuwa ya nemi kashe matarsa don ya ƙara jari a shagonsa

“Mama da baba na, ku yi hakuri, na yi haka ne saboda Allah bai amsa addu’ata ba, gwamma in mutu da in aikata zunubi, don Allah, ku gafarta mini, ina son ku, ku binne ni a gida.”

An tattaro cewa ɗaya daga cikin abokansa ya kai ziyara gidansa a ranar da lamarin ya faru amma ya tarar da ƙofar ɗakinsa a kulle.

Bayan an yi ta ƙwanƙwasa ƙofa ba tare da an ba da amsa ba, sai aka bude kofar da karfi, aka ga marigayin a rataye.

An gan bokitin fenti da babu komai a ciki wanda ake zargin ya kife ya hau ya rataya kansa a ɗakinsa.

Wani makwabcin ya bayyana marigayin wanda ya fito daga jihar Osun a matsayin musulmi mai kishin addini.

A halin da ake ciki, ɗaya daga cikin abokan aikinsa ya saka hoton bidiyo daga sallar jana’izar.

Leave a Reply