No menu items!

Sample Page Title

Date:

Uwargidan shugaban ƙasa ta raba jarin Naira miliyan 25 ga mata 500 a Katsina

Uwargidar Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, tare da haɗin gwiwar Gidauniyar Tony Elumelu, ta rabawa mata masu ƙananan sana’o’i 500 jari na Naira miliyan 25 a Jihar Katsina, inda kowacce mace ta samu Naira dubu 50.

An gudanar da taron rabon tallafin ne a yau Litinin a Katsina , da nufin bunƙasa tattalin arziki a matakin ƙasa.

KU KUMA KARANTA: Uwargidan shugaban ƙasa ta bayar da tallafin kuɗi ga waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa a Abuja

A yayin raba kuɗaɗen, uwargidar Gwamnan Jihar Katsina, Zulaihat Radda, ta ce shirin na da matuƙar muhimmanci ga al’umma.

“An kaddamar da wannan shiri a jihohi daban-daban na ƙasar nan domin tabbatar da cewa mata sun samu tallafin da suke buƙata don gina kyakkyawar makoma, ” in ji ta

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...