Uwargidan Shugaban Turkiyya ta ziyarci Najeriya don taron wayar da kai kan cutar kansa

0
25

Uwargidan Shugaban Turkiyya ta ziyarci Najeriya don taron wayar da kai kan cutar kansa

Mai ɗakin Shugaban Turkiyya, Emine Erdoga, na wata ziyara a Najeriya don wani gagarumin taro kan wayar da kai dangane da sankara da kuma shirin jan hankalin duniya kan cutar.

Mai Ɗakin Shugaban Najeriya Oluremi Tinubu ce ta tarbe ta a Abuja, babban birnin Najeriya.

“Akwai ƙarfafa gwiwa ganin irin yadda Nijeriya take ɗaukar nauyin ‘Shirin Wayar da Kai kan Sankara a Ƙungiyar Ƙasashe Musulamai na Afrika’ a bana, inda aka ɗora kan taron da aka yi a Istanbul a 2016 a matsayin wani ɓnagre na Babban Taron Muslunci na 13,” kamar yadda Mai Ɗakin Shugaban Turkiyya ta bayyana a cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafin X ranar Laraba.

KU KUMA KARANTA: Cutar sanƙarau ta kashe mutum 85 a Yobe

“Ina miiƙa godiyata ta musamman ga Misis Tinubu saboda jagorantar wannan muhimmin batu a Afirka, wanda yake da muhimmanci wajen samar da lafiya ba wai kawai a ƙasarta, har ma ga ƙasashen duniya.

Uwargidan shugaban ƙasar Turkiyya ta ƙara da cewa, “Ina fatan taron zai samar da sakamako mai kyau, kuma na yi imanin cewa hadin kan karfi da tausayi zai sa a kara wayar da kan jama’a.”

A nata ɓangaren, Uwargidan Shugaban Najeriya, Oluremi Tinubu ta ce: “Ina fatan sakamakon taron zai kasance mai amfani, na yi imanin cewa wayar da kan jama’a zai karu da karfi da haɗin kan zukata.”

Ministar Harkokin Mata ta Nijeriya Uju Kennedy-Ohanenye ta bayyana taron ƙara wa juna sanin a matsayin “abin yabawa.”

A cikin wata sanarwa da kungiyar ta OIC ta fitar a ranar Larabar da ta gabata ta ce, “Abin yabawa ne matuka da kungiyar OIC ta ci gaba da yin hadin gwiwa tare da cibiyoyinta da abokan huldar kasa da kasa don yin kokari sosai wajen samar da tsare-tsaren manufofin da suka dace don taimaka wa kasashe mambobin ƙungiyar wajen gina karfin kasa don yaki da cutar kansa,” in ji ta a cikin wata sanarwa a ranar Laraba.

Taron ƙara wa juna sani da aka gudanar a Abuja ya hada matan shugabannin kasashen Afirka 17 na kungiyar OIC. An yi shi ne don ƙirƙirar da haɓaka wayar da kan jama’a game da karuwar nauyin cutar kansa, musamman a Afirka.

Haka kuma yana bai wa matan shugaban kasa damar gano hanyoyin da za su kara inganta aikinsu na jagoranci da magance cutar yadda ya kamata domin ceton rayuka.

Mace-macen da cutar kansa ke haifarwa a Afirka sun ƙaru a cikin shekaru da yawa, tare da daukar matakan kariya da kariya, gami da manufofi da yakin wayar da kan jama’a.

A shekarar 2022, cutar daji ta kashe kusan mutum 573,650 a Afirka.

Leave a Reply