No menu items!

Sample Page Title

Date:

Turkiyya ta horar da sojojin ƙasar Gambia, wadda ke shirin karɓar baƙuncin taron Ƙungiyar Haɗin-kan Ƙasashen Musulmi OIC wanda za a gudanar a farkon watan Mayu.

Jumullar sojojin Gambia 351 ne suka samu horon na musamman ta ɓangarori da dama a Banjul babban birnin ƙasar, daga 7 zuwa 28 ga watan Afrilu.

Daga cikin horon da suka samu har da na naƙaltar yadda za su kare manyan baƙi.

Jakadan Turkiyya a Gambia Fahri Turker Oba da Ministan Harkokin Tsaro na Gambia Sering Modou Njie da Shugaban Sojojin Gambia Mamat Cham da sojoji da dama sun samu halartar wannan taro.

KU KUMA KARANTA: Hukumar CSDA ta horar da ma’aikata 886 a Zamfara

A lokacin taron, Oba ya bayyana cewa horon zai amfanar da sojojin na Gambiya kafin da kuma bayan taron.

Nijei a ɗayan ɓangaren, ya gode wa Turkiyya kan irin goyon bayan da take bayarwa domin ci gaban Gambia.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...