Connect with us

Rasuwa

Tsohon gwamnan Yobe, Bukar Abba Ibrahim, ya rasu

Published

on

Tsohon Gwamnan Jihar Yobe, Sanata Bukar Abba Ibrahim ya rasu yana da shekara 73.

Rahotanni sun ce ya rasu ne a ƙasar Saudiyya bayan ya yi fama da rashin lafiya.

Kafin rasuwarsa ya kasance gwamnan Jihar Yobe daga 1992 zuwa 1993, sannan ya sake jagorantar jihar a matsayin gwamna tun daga 1999 har zuwa 2007.

Marigayin ya wakilci Jihar Yobe a Majalisar Dattawan Najeriya daga 2007 har zuwa 2019.

Bukar Abba ya soma karatunsa na firamare a 1957. A 1965, sai ya tafi Kwalejin gwamnati ta Maiduguri domin ci gaba da karatun sakandare. Marigayin ya shiga Jami’ar Ahmadu Bello a 1972 inda ya samu digiri kan Quantity Surveying.

KU KUMA KARANTA: Shugaban ƙasar Namibia, Hage Geingob, ya rasu

Bayan nan sai ya ci gaba da digirinsa na biyu a Birtaniya tsakanin 1981 zuwa 1982.

Daga 1985 zuwa 1988 ya yi aiki a matsayin ma’aikacin gwamnatin jihar Borno inda har ya kai matakin kwamishinan ayyuka.

A Disambar 1991 watanni bayan Yobe ta samu jiha sai ya yi takarar gwamna inda ya ci zaɓe ƙarƙashin jam’iyyar SDP.

Ya riƙe wannan mukamin har zuwa lokacin da sojoji suka ƙwace iko da gwamnatin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Published

on

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Daga Ibraheem El-Tafseer

Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.

A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.

A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.

KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Continue Reading

Rasuwa

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Published

on

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Hajiya Zainab ta rasu ne a asibiti  bayan gajeruwar rashin lafiya.

Mutuwa ta riske ta ne a wani asibiti da ke Minna, babban birnin jihar a ranar Talata.

Gwamnan jihar, Mohammed Umaru Bago, ya bayyana alhini da game da wannan rashi.

Sakon ta’aziyyar da kakakinsa, Bologi Ibrahim, ya sa wa hannu ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga jihar.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Ya kuma yi addu’a Allah Ya sada ta da mafificin rahama a Aljanna Firdausi, Ya ba wa mijinta hakurin jure wannan rashi.

Continue Reading

Rasuwa

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Published

on

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Mahaifiyar tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff ta riga mu Gidan Gaskiya.

Mahaifiyar tsohon gwamnan, Hajja Aisa, ta koma ta Mahaliccinta ne a ranar Lahadi a Maiduguri, babban birnin jihar.

Ta rasu tana da shekaru 93, bayan fana da rashin lafiya.

Sanarwar rasuwar ta bayyana cewa za yi jana’izar Hajja Aisa da Azahar ranar Litinin 1 ga watan Yuli, 2024.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa tsohuwar jarumar Kannywood, Fati Slow rasuwa

Za a yi jana’izar ne a gidant Marigayi Galadima Modu Sheriff d da ke Damboa Road a Maiduguri.
Sanarwar ta kuma roka wa marigayiyar gafara da kuma Aljannatul Firdaus.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like