Connect with us

Labarai

Tsohon Gwamna El-Rufai ya zargi Buhari da sakaci wajen yaƙi da ta’addanci da ‘yan bindiga a Najeriya

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya zargi tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari da gazawa wajen daƙile ayyukan ta’addanci, yana mai cewa tsohon shugaban ya yi watsi da shawarar da ya ba shi na shawo kan rikicin.

Ya yi wannan jawabi ne a yayin bikin rantsar da magajinsa, Sanata Uba Sani, a Kaduna, ranar Litinin.

El-Rufai ya ce: “A shekarar 2017, na roƙi Gwamnatin Tarayya da ta ayyana ‘yan bindigar da suka kunno kai a matsayin ‘yan tayar da ƙayar baya, amma abin takaici, ba a yi haka ba sai 2022, bisa ga sanarwar da babbar kotun tarayya ta yi.

Abin takaici ne yadda Gwamnatin Tarayya ba ta yi la’akari da girman matsalar ba har sai da ‘yan bindigar suka yi ɓarnar rayuka, dukiyoyi, ’yanci da rayuwar mutane da dama.

KU KUMA KARANTA: Muna da ‘yancin mallakar muhalli don gudanar da rayuwarmu – Martanin almajiran Shaikh Zakzaky ga El-Rufai

“Duk da cewa an fara aikin soja tare da haɗin gwiwa a shekarar 2022, amma aikin bai cika ba.

Don haka, ina ƙira ga gwamnati da ta ci gaba da matsin lamba kan ‘yan bindiga, ‘yan tada kayar baya da ‘yan ta’adda, tare da sanya aikin soja ya zama cikakke kuma a lokaci guda a duk faɗin jihohi bakwai na gaba – shida a Arewa maso Yamma da Nijar – wadanda abin ya fi shafa.”

A martanin da El-Rufai ya mayar kan ƙalubalen da ya fuskanta a Kaduna, ya ce: “Gwamnatinmu ta yi aiki tuƙuru domin ganin ta daƙile ƙalubalen tsaro da ya kunno kai.

Matakan da muka ɗauka sun tabbatar da cewa ba mu samu wani rikici ba a faɗin jihar cikin shekaru takwas da suka gabata.”

A halin da ake ciki, sabon gwamnan ya yi ƙira da a samar da ‘yan sandan jihohi domin magance matsalar rashin tsaro a ƙasar.

Sani, a jawabinsa na farko, ya ce halin da ake ciki na buƙatar a sake duba dabarun. ya ce: “Jihar Kaduna ta samu kaso mai tsoka na zubar da jini da ɓarnar da ba dole ba.

Don haka, wannan gwamnatin za ta saka hannun jari sosai a duk wani yunƙuri da doka ta amince da su, gami da tura fasahar don tsaro da tabbatar da doka.

“Hakazalika, za mu taimaka wa ‘yan sanda, sojoji, jami’an tsaro da sauran hukumomin tsaro a jihar.

Har ila yau, za mu sa shugabannin gargajiya, cibiyoyin addini da shugabannin al’umma don tabbatar da ingantaccen tattara bayanan sirri, tare da yin aiki don samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsakanin al’ummomi daban-daban.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Shehu Sani ya caccaki El-Rufai saboda ya bar bashi mai yawa a jihar Kaduna | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like