No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tsaro: Gwamnan Kano ya ziyarci sansanin JTF a Tsanyawa da Shanono

Gwamna Abba Yusuf na Jihar Kano ya ziyarci sansanin rundunar haɗin gwiwa ta JTF a Karamar Hukumar Tsanyawa, inda ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro wajen magance barazanar tsaro da ta taso a yankin.

Gwamnan ya ce ziyarar tasa ta nufin tantance halin tsaro da ƙarfafa gwiwar jami’an tsaro, yana mai bayyana cewa ayyukan JTF za su dawo da zaman lafiya a yankunan da suka gamu da hare-hare.

KU KUMA KARANTA: Taron Gwamnonin Arewa Maso Gabas: Dole ne mu ƙarfafa haɗin kai don dakatar da matsalar tsaro – Gwamna Buni

Ya jaddada cewa gwamnatinsa za ta ba da dukkan goyon baya, musamman a fannin jin daɗin jami’an tsaro da samar da kayan aiki, tare da tabbatar da cewa waɗanda aka sace za a kubutar da su cikin koshin lafiya.

Shugaban rundunar ta 3 na Sojan Najeriya, Birgediya Janar Ahmed Tukur, ya bayyana cewa rundunar ta ƙunshi jami’an soji, rundunar sojan sama, ‘yansanda, DSS, NSCDC da ‘yan sa-kai, kuma suna gudanar da ayyuka a wuraren da ake fama da barazana.

Gwamnan ya kuma ziyarci kauyen Yankamaye, inda aka sace mutane shida tare da kashe wata tsohuwa.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...