Connect with us

Labarai

Tsadar Rayuwa: Gwamnatin Tarayya za ta fara rabon hatsi

Published

on

Gwamnatin Tarayya za ta fara rabon hatsi a faɗin ƙasar nan, domin rage wahalar tsadar rayuwa da ake fuskanta a Najeriya.

Ministan Noma da Samar da Abinci, Sanata Abubakar Kyari ne, ya wallafa hakan a shafinsa na X (Twitter), a ranar Litinin.

“A wannan yanayi da ake ciki, ina mika jaje na ga wadanda wahalar da ake ciki ta shafa a kasar nan. Na fahimci girman al’amarin, musamman ga waɗanda ba su da abin yi.

“Ina so na tabbatar muku cewa sadaukarwar da muka yi don jin daɗinku ba za ta tashi a banza ba. Za mu fara rabon tan 42,000 na hatsi, kamar yadda mai girma shugaban kasa, ya amince a faɗin jihohi 36 na tarayyar Najeriya don rage raɗaɗin halin da ake ciki.

KU KUMA KARANTA: Ƙungiyar NLC ta gudanar da zanga-zanga, saboda tsadar rayuwa a faɗin Najeriya

“Muna aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumar NEMA da kuma DSS domin ganin cewa hatsin ya kai ga wadanda suka dace su rabauta. Bugu da kari kuma, za a sake fitar da tan 58,500 na shinkafa zuwa kasuwa domin daidaita farashin kayan abinci.”

Ministan, ya roki ’yan Najeriya da su mara wa gwamnatin shugaba Tinubu baya a yunkurinta na magance kalubalen da ƙasar ke fuskanta.

“Na san irin halin da al’ummar Najeriya ke ciki, kuma na san wannan shugaban zai jagorance mu a halin da muke ciki. Mu tashi tsaye domin mara wa shugaban kasa baya a kokarinsa na ganin Najeriya ta inganta,” in ji Kyari.

“Gwamnatinmu a karkashin jagorancin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ta himmatu wajen magance waɗannan kalubale da kuma yin aiki don samar da makoma mai tsaro da wadata ga kowa a ƙasar nan.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like