Connect with us

Labarai

Tsadar abinci: Gwamnati za ta fara raba kayan abinci a faɗin Najeriya – Kwamiti

Published

on

Gwamnatin Najeriya za ta fara ɗaukar matakin rage matsalar rashin abinci da tsadarsa a faɗin ƙasar biyo bayan ƙorafe-ƙorafe da zanga-zangar da aka yi a wasu sassan ƙasar kan tsadar rayuwa.

Za’a raba ton 42 na kayayyakin abinci iri-iri waɗanda za a fitar daga runbunan ajiye abincin baya ga shinkafa tirela 2000 da za a sayo daga wurin ‘yan kasuwa don rabawa ma jama’a. Wannan bayanin ya fito ne daga wurin kwamitin Ministoci da sauran manyan jami’an gwamnati da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kafa biyo bayan ƙorafe-ƙorafe rashin abinci da kuma tsadarsa a faɗin Najeriya.

Kwamitin ya yanke wannan shawarar ce bayan zaman da ya yi na kwanaki uku don tattaunawa kan hanyoyin da za a ɓullo ma matsalar ƙarancin abinci da kuma tsadarsa a Najeriya.

KU KUMA KARANTA:Najeriya ta ƙara shiga yanayin ƙarin haraji bayan cire tallafin Fetur

Mamban kwamitin kuma Ministan Yaɗa Labaran Najeriya, Alhaji Muhammad Idris, wanda bayan zaman kwamitin na uku ya yi ƙarin bayani a manema labarai.

To amma Shugaban Kungiyar Manoma ta Najeriya, Alhaji Kabiru Ibrahim Faskari, ya ce ya kamata a haɗa irin wannan matakin da tsarin tallafa ma manoma da na’urorin zamani a farashi mai rahusa kuma ya zama tsari ne na dindindin ba sau ɗaya kawai ba ko kuma idan ta ɗauro kawai ba. Ya ce kodayake gwamnati ba ta da isasshen kuɗin da za ta tallafa ma mutane da kayan abinci kyauta, ya kamata shi ma kayan abincin a sayar ma talakawa a farashi mai rahusa.

Minista Idris ya gargaɗi ‘yan kasuwa da ke sayen kayan abinci su kuma ɓoye don su sayar daga baya da matuƙar tsada da su daina. Ya ce gwamnati ta san irin waɗannan ‘yan kasuwa kuma idan ta kama za ta ɗau mataki a kan su.

Ya ce tun da bayar wa kyauta na iya janyo rubibi da ruɗani a wuraren raba abincin, sayarwa a farashi mai rahusa zai ɗan rage rubibi da hargowa. Ya kuma ce ya kamata gwamnati ta tabbatar waɗanda ke matuƙar buƙata aka fi bai wa fifiko wajen rabawa, ba magoya bayan jam’iyya ba. Kuma a tabbatar duk wanda aka ba shi abincin bai sayar ba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like