Connect with us

Labarai

Tinubu ya yabawa INEC, ya miƙa godiyarsa ga ‘yan Najeriya

Published

on

“‘Yan uwana ‘yan Nigeria Ina matukar ƙasƙantar da kai duba da zaɓe na da ku kayi na zama shugaban ƙasa na 16 na ƙasarmu abin ƙaunarmu.

“Wannan lokaci ne mai haske a rayuwar kowane mutum da kuma tabbatar da wanzuwar dimokuraɗiyyarmu.

“Daga zuciyata nace na gode, ko kai mai goyon baya na ne ko mai goyon bayan Atiku, ko kuma mai goyon bayan Obi ne ko kuma kai ɗan Kwankwasiyya, duk na gode maku, ko da kuwa da wacce siyasa kake da alaƙa, ka zaɓi al’umma ta gari, mai fatan alheri, ina kuma gode maka da irin gudummawar da ka bayar da kuma sadaukar da kai ga dimokuraɗiyyarmu.

“Kun yanke shawara da amanarku ga manufofin dimokuraɗiyya na Najeriya da aka kafa bisa wadata tare da wanda aka raya ta aƙidar haɗin kai, adalci, zaman lafiya da haƙuri. Sabon fata ya kunno kai a Najeriya.

” Muna yaba wa INEC kan gudanar da zaɓe na gaskiya da adalci, abubuwan da suka faru ba su da yawa a adadi kuma ba su da mahimmanci ga sakamako na ƙarshe, tare da kowane zagaye na zaɓe, muna ci gaba da kammala wannan tsari mai mahimmanci ga rayuwar dimokuraɗiyyarmu.

“A yau, Najeriya ta tsaya tsayin daka a matsayin katafariyar ƙasa a Afirka, tana ƙara haskakawa a matsayin babbar dimokuraɗiyya a nahiyar, ina godiya ga duk wadanda suka goyi bayan yaƙin neman zabena.

KU KUMA KARANTA: 2023: Yadda Tinubu ya lashe zaɓen shugaban ƙasa

“Daga shugaba Buhari wanda ya jagoranci yaƙin neman zaɓe na a matsayina na shugaban kungiyar, har zuwa mataimakina ɗan takarar shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima.

“Zuwa ga Gwamnonin ci gaba na jam’iyyarmu da na wannan ƙasa, zuwa ga shugabancin jam’iyya, ga ‘yan jam’iyyarmu masu biyayya, kuna bina bashin godiya,ga ɗaukacin ƙungiyar kamfen, ina gode muku da gaske.

“Ina godiya ga matata mai ƙauna da dangina masoyana waɗanda tallafinsu ya ƙarfafa min gwiwa, idan ba tare da ku ba, wannan nasarar ba za ta yiwu ba.l, ina godiya ga Allah Madaukakin Sarki, wanda da rahamar sa ne aka haife ni ɗan Nijeriya kuma ta dalilinsa maɗaukakin manufa na tsinci kaina a matsayin wanda ya lashe wannan zaɓe, ina addu’a Allah Ya ba ni hikima da jajircewa wajen jagorantar al’umma zuwa ga daukakar da Shi kadai ya kaddara mana.

“A ƙarshe ina gode wa al’ummar Najeriya bisa yadda suka yi imani da dimokraɗiyyar mu, zan zama shugaba mai adalci ga dukkan ‘yan Najeriya, zan kasance daidai da burinku, in ba da kuzarinku da amfani da basirar ku don isar da al’ummar da za mu yi alfahari da ita.

“Ga ‘yan takara, tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku, tsohon gwamna Kwankwaso, tsohon gwamna Obi da sauran su, ina miƙa hannun sada zumunci,wannan ya kasance gasa, kamfen mai girma.

“Kuna da matuƙar girmama a idona, dole ne a yanzu gasar siyasa ta ba da damar yin sulhu a siyasance da gudanar da mulki mai dunkulewa tare.

“A lokacin zabe, watakila ka kasance abokin hamayya na amma ba ka taɓa zama makiyi na ba, a cikin zuciyata ku ‘yan’uwana ne.

“Duk da haka, na san wasu ‘yan takara zai yi masu wuya su amince da sakamakon zaɓen, haƙƙin ku ne ku nemi hanyar shari’a, abin da ba daidai ba ne ko abin da ba shi da kariya ba, shi ne kowa ya shiga tashin hankali.

“Duk wani kalubale ga sakamakon zaben ya kamata a gabatar da shi a gaban kotu, ba a kan tituna ba,ina kuma rokon magoya bayana da su bar zaman lafiya ya ɗure, mun gudanar da yakin neman zabe mai tsari, cikin lumana da ci gaba.

“Dole ne sakamakon yaƙinmu ya kasance mai kyau. Eh, akwai rarrabuwa a tsakaninmu da bai kamata ba, mutane da yawa ba su da tabbas, suna da fushi da rauni; ina isa ga kowane ɗayanku da muyi haƙuri da juna.

“Bari ingantattun bangarorin dan Adam mu su ci gaba a wannan lokaci mai muni, mu fara warkewa da kwantar da hankalin al’ummarmu,yanzu a gare ku matasan kasar nan, ina jin ku da babbar murya na kuma fahimci raɗaɗin ku, burinku na kyakkyawan shugabanci, tattalin arziki mai kyau da kuma ƙasa mai aminci wacce za ta kare ku da makomarku.

” Ina sane da cewa a gare ku da yawa Najeriya ta zama wurin da ake fama da ƙalubalen da ke tauye wa kanku kyakkyawar makoma, gyaran gidanmu na kasa mai daraja yana bukatar ƙoƙarin mu da juna, musamman ma matasa.

“Yin aiki tare, za mu ciyar da wannan al’umma ba kamar da ba, mataimaki na, zaɓaɓɓen shugaban ƙasa Shettima, da na fahimci ƙalubalen da ke gabanmu,mafi mahimmanci, muna kuma fahimta kuma muna matuƙar daraja hazaka da nagartar ku, al’ummar Najeriya.

“Mun yi alƙawarin saurare da yin abubuwa masu wuya, manyan ayyuka, waɗanda suka dora mu a kan turbar ci gaba mai ɗurewa, riƙe kanmu da tabbaci, amma da fatan za a ba mu dama tukuna.

“Tare, za mu gina al’umma mai haske da fa’ida don yau, gobe da shekaru masu zuwa, a yau kun ba ni mafi girman girma da za ku iya ba wa mutum ɗaya, kuma a sakamakon haka, zan ba ku iyakacin ƙoƙarina a matsayin shugabanku na gaba kuma babban kwamandan ku.

“Zaman lafiya da haɗin kai da wadata su ne ginshikan al’ummar da muke son ginawa.

“Lokacin da kuka kalli abin da za mu cim ma a cikin shekaru masu zuwa, za ku yi magana da alfahari da kasancewa ‘yan Najeriya.

“Na gode muku duka. Allah ya saka muku da alkhairi. Allah ya taimaki tarayyar Nigeria” in ji zaɓaɓɓen shugaban ƙasa. Bola Ahmed Tinubu.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Nasarar Tinubu daga Allah ne – Aisha Buhari | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Published

on

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Afirka ta Yamma mai rarrabuwan kai ta gudanar da tarukan ƙolin shugabannin ƙasa guda biyu a ƙasashe daban-daban biyu a ƙarshen makon, inda aka gudanar da taro farko ranar Asabar a Nijar tsakanin shugabannin mulkin soja na yankin Sahel.
A gefe guda kuma za a gudanar da wani taron ƙoli ranar Lahadi a Najeriya inda shugabannin sauran ƙasashe mambobin ƙungiyar tattalin arziƙin yankin ta ECOWAS za su hallara.

Taron ƙolin da ake yi yau Asabar a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar, zai kasance karo na farko tsakanin shugabannin sojojin sabuwar ƙungiyar haɗin kan yankin Sahel wato Alliance of Sahel States ko kuma AES.

Mali, Burkina Faso da Nijar su ne suka kafa yarjejeniyar kare juna a watan Satumba, waɗanda suka bar babbar ƙungiyar ECOWAS a cikin watan Janairu.

Ficewar su daga ECOWAS, wani ɓangaren ya samo asali ne daga zargin da suke yi cewa Paris tana yiwa ƙungiyar katsalandan kana ba ta ba da taimakon da ya kamata a yaƙi da masu iƙirarin yaƙin jihadi.

Ficewar ta sa ƙasashen uku sun janye kansu daga Faransa da ta yi musu mulkin mallaka, suka kori sojojin Faransa masu yaƙi da masu iƙirarin jihadin kana suka juya zuwa ga ƙasashen da suke ƙira da aminan gaskiya, da suka haɗa da Rasha da Turkiya da kuma Iran.

KU KUMA KARANTA:Shugabannin Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa ƙungiyar haɗaka

Idan aka yi la’akari da munanan tashe-tashen hankula na ‘yan jihadi da ƙasashen uku ke fuskanta, “yaƙin da ta’addanci” da “ƙarfafa haɗin gwiwa” za su kasance kan ajandar taron ƙolin na yau Asabar, a cewar fadar shugaban ƙasar Burkina Faso.

Taron ƙolin da za a gudanar ranar Lahadi a Abuja zai ba shugabanni a ƙasashen ECOWAS damar tattaunawa a kan irin alaƙa da za su ƙulla da ƙungiyar ta AES.

Bayan wasu tarurrukan da suke yi tsakanin ƙasashe biyu, shugabannin uku na yankin Sahel sun yi taro a karon farko tun bayan da suka hau karagar mulki ta hanyar juyin mulki tsakanin shekarar 2020 zuwa 2023.

Continue Reading

Labarai

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Published

on

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

 

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewar ‘yan Najeriya miliyan 82, kimanin kashi 64 na ‘yan ƙasar ka iya fuskantar matsalar yunwa nan da shekarar 2030.

Haka kuma MƊD ta yi ƙira da gwamnatin ƙasar ta magance matsalar sauyin yanayi da matsalar ƙwari da sauran abubuwan da yi wa harkar noma barazana.

Jaridun Najeriya sun ambato jami’in Majalisar Ɗinkin Duniyar, Taofiq Braimoh – wanda ya wakilci kodinetan ayyukan jin ƙai na hukumar abinci da ayyukan noma na majalisar na bayyana haka lokacin da yake jawabi kan matsalolin ƙarancin abinci a taron ƙaddamar da shirin bunƙasa ayyukan noma na ‘CropWatch’ a birnin Abuja.

KU KUMA KARANTA:Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi maraba da sakin yara 21 da aka yi garkuwa da su

Mista Braimoh ya ce akwai buƙatar gwamnatin Najeriya ta ɗauki matakan da suka dace cikin gaggawa don magance matsalar.

“Gwamnatin Najeriya tare da haɗin gwiwa masu ruwa da tsaki, sun gudanar da bincike na shekara-shekara da suka saba gudanarwa kan abinci. Sakamakon binciken ya tayar da hankali, kimanin mutum miliyan 82 ne za su fuskanci yunwa nan da 2030,” kamar yadda Jaridun ƙasar suka ambato Braimoh na bayyanawa.

Ya ci gaba da cewa matsalar rashin abinci da ƙasar ke fama da shi, baya rasa nasaba da matsalar sauyin yanayi da duniya ke fama da ita, da matsalar ƙwari da wasu abubuwa da ke yi wa harkar noma barazana a ƙasar.

Hasashen na Majalisar Ɗinkin Duniyar na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsadar abinci, lamarin da ya tilasta wa gidaje da dama haƙura da sayen abincin da suka saba ci.

A cikin rahotonta baya-bayan nan, hukumar ƙididdigar ƙasar ta ce farashin abinci a ƙasar ya ƙaru zuwa kashi 40.66 a watan Mayu, matakin da aka jima ba a ga irinsa ba.

Continue Reading

Labarai

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Published

on

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta maka jaridar Daily Trust a kotu, tare da shigar da ƙorafi game da ita, a gaban ƙungiyar masu gidajen jarida ta Najeriya saboda abin da ta ƙira ”yaɗa kalaman neman tayar da rikici da karya aikin jarida”

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tana sane da yadda a cikin ‘yan watannin baya, jaridar Daily Trust ke yaɗa labaran da ke neman gogawa gwamnatin kashin kaji.

Da ya ke magana a wajen wani taron manema labarai a ranar Asabar, ministan yaɗa labaran ya kafa hujja da labaran da jaridar Daily Trust ta wallafa a game juyin mulkin Nijar, da wanda ya ce jaridar ta rubuta a kan shirin sauya sunan titin Murtala Muhammad da ke Abuja zuwa Wole Soyinka da kuma na baya bayan nan a game da sanya hannu a kan yarjejeniyar da ta shafi amincewa da auren jinsi.

KU KUMA KARANTA: Alaƙar soyayya tsakanin jinsi ɗaya ta haramta a Iraƙi

Ya yi bayanin cewa a dukkan labaran, gwamnatin ta gano yadda jaridar ta bayar da rahoto ba tare da gabatar da hujja ko shaidun zargin da ta yi ba, lamarin da kuma gwamnatin ke kallo a matsayin wani yunƙuri na wallafa ƙarya domin tunzura jama’a.

Ya ce: ‘’Ba mu taɓa tunanin Daily Trust da mutanen da ke da ita za su kai wannan mataki ba wajen neman tayar da rikici a ƙasar nan, ta hanyar zargin cewa gwamnati ta sanya hannu a kan yarjejeniyar tallata auren jinsi. Wannan tsabar zalunci ne saboda babu wannan tanadi a cikin yarjejeniyar.’’

Ministan ya koka da yadda wannan labarin ya janyo huɗuba mai zafi daga wasu malaman addini da kuma jefa jama’a cikin halin ɗarɗar, wanda kuma ya ce jaridar ce ta janyo.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Saboda haka, ministan ya ce ‘’Gwamnatin tarayya za ta bi duk hanyoyin da doka ta amince da su, domin neman haƙƙi a kotu.’’

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like