Connect with us

Labarai

Tinubu ya rattaɓa hannu kan ƙudirin ba da lamuni a ɗaliban manyan makarantu

Published

on

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rattaɓa hannu kan ƙudirin ba da lamuni na ɗalibai ya zama doka, wanda wani ɓangare ne na alƙawuran yaƙin neman zaɓensa.

Dokar za ta bai wa ɗalibai marasa galihu na manyan makarantu damar samun lamuni na Gwamnatin Tarayya na tsawon lokacin karatunsu.

Dele Alake, mai magana da yawun shugaban ƙasar ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a ƙarshen rattaɓa hannun a fadar shugaban ƙasa, dake Abuja.

Alake ya ce ƙudirin dokar zai bunƙasa neman ilimi na matasa a faɗin ƙasar, inda ya ƙara da cewa domin jin daɗin wurin, dole ne ɗalibai su nuna alamun rashin wadata.

Ya ce za a kafa wani kwamiti da aka zaɓo daga dukkan masu ruwa da tsaki a harkar ilimi domin tafiyar da yadda za a gudanar da yadda za a fitar da basussukan yadda ya kamata.

KU KUMA KARANTA: Cire tallafin mai: Za mu sakawa ‘yan Najeriya da manyan ayyukan jin daɗin rayuwa – Tinubu

Alake ya ce za a yi amfani da kaso na kuɗaɗen shiga na tarayyar ne wajen ɗaukar nauyin wannan sabon shiri.

Andrew Adejo, Babban Sakatare a Ma’aikatar Ilimi, ya ce dokar za ta tsaya tsayin daka kan matsalar ƙarancin kuɗaɗe da ke kawo cikas ga neman ilimi.

Ya ce rattaɓa hannu kan ƙudirin na nuni da yadda gwamnatin Tinubu ta ƙudiri aniyar tafiyar da batun ilmin inganci da ƙididdiga a zamaninta.

Adejo ya ce ma’aikatar ta riga ta samu gogewa a fannin harkokin kuɗi ta hanyar tsarin hukumar bayar da tallafin karatu ga ɗalibai.

Ya ƙara da cewa yadda ƙasar ke tafiyar da lamuni a ayyuka daban-daban kuma zai taimaka wajen ƙwato rancen.

Ya ƙara da cewa za a bayar da lamunin da ba ruwa ne bisa la’akari da yawan shekarun da ɗaliban suka yi karatu da kuma yadda za su iya biya.

Sakatare na dindindin ya ce ya kamata kafafen yaɗa labarai su taimaka wajen yaɗa bayanai kan batun tallafin ilimi a ƙasar.

Ya ce ya kamata jihohi su yi tattaki na tallafin kuɗi da fasaha na gwamnatin tarayya domin baiwa ‘yan Najeriya ilimi mai inganci.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like