Connect with us

Labarai

Tinubu ya naɗa ɗan Ganduje darakta a hukumar lantarki ta REA

Published

on

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa Umar Abdullahi Umar, ɗan tsohon Gwamnan Kano kuma Shugaban jam’iyyar APC na Kasa, Abdullahi Umar Ganduje a matsayin ɗaya daga cikin manyan daraktocin Hukumar Samar da Wutar Lantarki a Karkara (REA).

Wannan dai na zuwa ne bayan da shugaban ƙasar ya dakatar da shugaban hukumar, Ahmad Salihijo Ahmad.

Dakatarwar ta sai abin da hali ya yi ta kuma haɗa da wasu manyan daraktoci uku na hukumar kamar yadda wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Ajuri Ngelale ya fitar ta nuna.

Sanarwar da Mista Ngelale ya fitar a yammacin wannan Alhamis ɗin, ta ce sauran manyan jami’an hukumar uku da dakatarwar ta shafa sun haɗa da Olaniyi Alaba Netufo da Barka Sajou da Sa’adatu Balgore.

Tinubu ya kuma bayar da umarnin gudanar da bincike kan jami’an dangane da zargin karkatar da dukiyar hukumar ta fiye da naira biliyan 1.2 a ɗan tsukukun shekaru biyu da suka gabata.

KU KUMA KARANTA: Ministan Lantarki na Najeriya ya yi barazanar ƙwace lasisin kamfanonin rarraba wuta

Bayanai sun ce hukumomin yaƙi da rashawa sun soma tatso wani kaso daga cikin kuɗin da ake zargin manyan jami’an sun yi ruf da ciki a kai.

Tuni dai shugaban ƙasar ya maye gurbinsu da sabbin shugabanni da suka haɗa da Abba Abubakar Aliyu a matsayin Manajan Darakta na hukumar ta REA.

Sauran waɗanda shugaban ƙasar ya naɗa a matsayin manyan daraktocin da za su maye gurbin waɗanda ya dakatar sun haɗa da Ayoade Gboyega da Umar Abdullahi Umar da Doris Uboh da kuma Olufemi Akinyelure a matsayin shugaban sashen kula da manyan ayyukana hukumar.

Ngelale ya ambato shugaban ƙasar na cewa ana kyautata zaton dukkan waɗanda aka yi wa sabbin naɗin za su sauke nauyin da rataya a wuyansu cikin gaskiya da rikon amana.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like