No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tinubu ya kawar da matsalar rashin biyan albashi a jihohi 27 — Ministan Yaɗa Labarai

Daga Jameel Lawan Yakasai

Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, ya bayyana cewa sauye-sauyen da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aiwatar sun kawo ƙarshen matsalar biyan albashi a jihohi 27.

Ya yi wannan bayani ne a Abuja yayin da kwamishinonin yaɗa labarai daga jihohi 36 suka kai masa ziyara.

Idris ya ce manufofin shugaban suna tafiya ne don amfanin ƙasa baki ɗaya, ba siyasa ba, tare da tabbatar da cewa ayyuka suna gudana a dukkan jihohi ba tare da nuna bambanci ba.

Ministan ya ce cire tallafin man fetur ya buɗe sabbin hanyoyin samun kuɗaɗe ga jihohi, wanda ya taimaka musu wajen aiwatar da muhimman ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Babu Farfesan da albashinsa yake kai shi wata – Farfesa Balarabe Abdullahi

Ya ƙara da cewa kafin Tinubu hauhawa mulki, kaso 97 cikin 100 na kuɗaɗen shiga na tarayya ana amfani da su wajen biyan bashi, abin da ya hana jihohi biyan albashi yadda ya kamata.

Idris ya yi kira ga gwamnatocin jihohi da su yi aiki tare da shugaban kasa wajen tabbatar da cigaban ƙasa. Haka kuma ya sanar da cewa ma’aikatarsa za ta kai ziyara zuwa wasu jihohi domin duba ayyukan da ake yi da kuma jin ra’ayin jama’a.

Shugaban taron kwamishinonin yaɗa labarai, Usman Tar daga jihar Borno, ya ce sun yi alkawarin inganta haɗin kan ƙasa ba tare da la’akari da jam’iyya ko bambancin siyasa ba.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...