No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tinubu ya karɓi baƙuncin shugaban Senegal, Bassirou Faye

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya karɓi baƙuncin Shugaban Senegal, Bassirou Diomaye Faye a fadar Aso Rock da ke Abuja.

Wannan shi karo na farko da shugaban mafi ƙarancin shekaru a nahiyyar Afirka ya kawo ziyara Najeriya tun bayan zamansa Shugaban Senegal a watan Afrilun da ya gabata.

Bayanai sun ce Bassirou Diomaye Faye mai shekaru 44 ya zo ziyarar aiki ne a Najeriya.

Sai dai zuwa babu masaniya a kan aikin da ya kawo Shugaban Senegal ɗin Najeriya.

A watan Afrilu da ya gabata ne aka rantsar Bassirou Diomaye Faye a matsayin shugaban Senegal.

KU KUMA KARANTA: Majalisa ta amince wa Tinubu ciyo bashin $500m don sayen mitocin lantarki

An rantsar da ɗan jam’iyyar adawar bayan ya ni nasara da kashi 54 cikin ɗari na kuri’un da aka kaɗa a zaɓen a kan abokin hamayyarsa na hadakar jam’iyyu masu mulki.

Tinubu, wanda shi ne shugaban ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen yammacin Afirka (ECOWAS), ya karɓi bakuncin Bassirou Faye tare da wasu ƙusoshin gwamnatin ƙasar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...