No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tinubu ya je Kano ta’aziyyar marigayi Alhaji Aminu Ɗantata

Daga Shafaatu Dauda

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya je jihar Kano a ranar juma’a domin yin ta’aziyyar rasuwar hamshaƙin ɗan kasuwar nan Alhaji Aminu Alhassan Ɗantata.

Jirgin da ya ɗauko Tinubu da muƙarrabansa ya sauƙa a filin jirgin saman Aminu Kano da ke Kano da misalin karfe uku na yammacin ranar Juma’a.

KU KUMA KARANTA: Ta’aziyyar Ɗantata: Jagororin Jam’iyyar APC a Kano sun ƙauracewa tarbar Kashim Shattima

Ya samu tarba daga tawagar da suka haɗa da jami’an gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Yusuf da jiga-jigan jam’iyyar APC na jihar Kano.
Idan za a iya tunawa Alhaji Aminu Ɗantata ya rasu makonni uku da suka gabata lokacin da Tinubu ba ya ƙasar.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...