Connect with us

Labarai

Tinubu ya dakatar da shirin N-Power da wasu shirye-shiryen rage raɗaɗin talauci

Published

on

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da dukkan shirye-shiryen da ake gabatarwa ƙarƙashin Hukumar Kula da Shirin Tallafa wa Marasa Galihu na ƙasa (NSIPA), in ji Gwamnatin Tarayyar ƙasar.

Da yake sanar da dakatar da shirye-shiryen a ranar Juma’ar nan, Daraktan Watsa Labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Segun Imohiosen ya ce matakin na shugaban “na daga ayyukan bincike kan zargin almundahana wajen kula da hukumar.”

Sanarwar ta ce “An dakatar da dukkan shirye-shirye huɗu da Hukumar ke gabatarwa na N-Power, Shirin Aika Kuɗaɗe Kai-Tsaye, Shirin ƙarfafawa Mutane da Koya Sana’o’i na Gwamnati da Ciyar da ɗaliban Makarantu na tsawon makonni shida a karon farko.”

“Shugaba Tinubu ya kuma bayyana matuƙar damuwa game da ayyukan rashin dacewa da cuwa-cuwa a biyan kuɗaɗen a ƙarƙashin shirye-shiryen.”

KU KUMA KARANTA: Shugaba Tinubu ya dakatar da Ministar Ma’aikatar Jin-ƙai, Betta Edu

Kamar yadda sanarwar ta bayyana, Shugaba Tinubu ya kuma kafa kwamitin ministoci da zai yi zuzzurfan nazari kan ayyukan hukumar, tare da bayar da shawarwarin kawo gyara a NSIPA.

A tsawon lokacin dakatar da shirin, duk wasu ayyuka da suka shafi Hukumar NSIPA sun tsaya cak, in ban da raba kayayyaki, gudanar da shirye-shirye, haɗin gwiwa da yin rajista.

Tinubu ya kuma tabbatarwa da ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa ta mayar da hankali wajen tabbatar da aiki da tsari na adalci, kuma daga yanzu za a tabbatar da an aiwatar da shirin tallafa wa jama’a ta yadda ya kamata, za a taimaka wa ‘yan Nijeriya mabukata.

Bayan damuwa kan yadda ake mu’amala da kuɗaɗe a hukumar, Shugaba Tinubu a ranar 2 ga Janairu ya dakatar da shugabar Hukumar Kula da Shirin Tallafa wa Marasa Galihu ta Ƙasa (NSIPA), Halima Shehu.

Kafin naɗa Halima a wannan matsayi, ta yi aiki a matsayin Jagorar Shirin Tura Kuɗaɗe Kai-Tsaye, kuma a baya ma ta yi aiki da Ma’aikatar Harkokin Jinkai, Yaƙi da Annoba da Ci-gaban Zamantakewa ta Tarayya.

Bayan dakatar da Halima, an naɗa Babban Jami’in Shirin N-Power Dr Akindele Egbuwalo a matsayin shugaban riƙo har zuwa lokacin da za a kammala bincike.

Dakatarwar tata ta zo watanni uku bayan Majalisar Dattawa ta tabbatar da ita a matsayin shugabar Hukumar NSIPA.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like