No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tinubu ya buƙaci Gwamnan Kano ya shiga tsakani kan rikicin Rimin Zakara

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bukaci Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano da ya shiga tsakani a rikicin filaye tsakanin Jami’ar Bayero, Kano (BUK) da al’ummar kauyen Rimin Zakara da ke makwabtaka da ita don ganin an maidowa jami’ar filayen ta.

Shugaban kasar ya yi wannan kira ne a jiya Asabar yayin bikin yaye dalibai karo na 39 na jami’ar.

Tinubu, wanda karamar Ministan Harkokin Ilimi, Farfesa Suwaiba Ahmed, ta wakilta, ya bukaci Gwamnan da ya shiga lamarin ta hanyar maidowa da jami’ar takardun mallakar fili da su ke hakkin ta ne

KU KUMA KARANTA:Mulki ba zai koma arewa ba sai Tinubu ya kammala shekaru 8 – Abdullahi Ganduje

Ya kuma ce gwamnati na da masaniya kan kalubalen rashin shinge da jami’ar ke fuskanta, kuma ta samar da wasu kudade don gina shinge a kewayenta.

Shugaban kasar ya kuma bukaci jami’o’in kasar da su yi amfani da hanyoyin nazari da bincike don samar da hanyoyin samun wutar lantarki mai zaman kan ta domin rage kashe makudan kudade wajen samar da wuta a jami’o’i.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...