No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Tawagar gidan Rediyon jihar Yobe (YBC) ƙarƙashin jagorancin babban Manajanta, Alhaji Isah Galadima, ta kai ziyarar ta’aziyya ga Dakta Hassan Gimba, Mawallafi kuma shugaban gidan jaridar Neptune Prime Network.

Da suke jajantawa, sun miƙa ta’aziyyarsu bisa rasuwar Hajiya Hafsat Ahmed Gimba, tare da bayyana rasuwarta a matsayin wani babban giɓi, ba ga ’ya’yanta kawai ba, rashi ne ga dukkan al’umma.

Da yake ƙarin haske game da irin tasirin da Hajiya ta yi ga al’umma, yana mai jaddada cewa rasuwarta rashi ce ba ga ‘ya’yanta tara da danginta kaɗai ba, har ma ga al’umma da kuma bil’adama baki ɗaya.

Hakazalika, masu watsa shirye-shiryen sun yarda da mahimmancin rayuwar da aka kashe da kuma dawwamammen gadon da ta bari.

KU KUMA KARANTA: Mahaifiyar Mawallafin Neptune Prime, Hassan Gimba, ta rasu tana da shekara 85

Daga ƙarshe suka yi addu’a ga Dakta Hassan Gimba da iyalansa, tare da addu’ar Allah ya jiƙan mahaifiyarsu da ta rasu.

Tawagar YBC ɗin, sun haɗa da Dakta Ahmed Bedu, tsohon shugaban NUJ na jihar Yobe, Malami a jami’ar Maiduguri. Sai daraktan kula da ma’aikata da gudanarwa; Alhaji Yerima Ahmed Saleh; Umar Mohammed Gaidem, Daraktan shirye-shirye; Mallam Habu Isa Sabon Layi, Mataimakin Daraktan Labarai; Baba Garba Alhaji, Babban mai kula da ɗakin ajiya; da Hassan Sama’ila.

Idan za a iya tunawa, an binne gawar Hajiya Hafsat Ahmed Gimba a ranar 8 ga watan Janairun 2024, a maƙabartar NEPA da ke ƙaramar hukumar Potiskum a jihar Yobe.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...