Connect with us

Ƙasashen Waje

Tarihin sabon shugaban ƙasar Senegal, Bassirou Diomaye Faye

Published

on

An haifi Diomaye Faye a ranar 25 ga Maris na 1980, a ƙauyen Ndiaganiao da ke yankin Thies na ƙasar Senegal.

Ya yi karatun digiri na biyu a fannin shari’a, kuma ya gama digirin farko a Makarantar Ƙasa ta Nazarin Gudanarwa da Mulki. A 2007 ya fara aiki da Hukumar Tattara Haraji ta Ƙasa.

A 2014, ya kafa jam’iyyar Pastef ta ‘Ƴan Kishin Afirka.

An kama shi a ranar 14 ga watan Afrilun 2023 tare da zarginsa da laifin “daƙile ayyukan jami’an tsaro” bayan ya yi watsi da tsarin shari’ar da aka bi wajen hukunta uban gidansa Ousmane Sonko.

KU KUMA KARANTA: Ɗan takarar jam’iyyar adawa Bassirou na kan gaba a zaɓen Senegal

Sakamakon yadda ba a taɓa tuhumar sa da aikata babban laifi, ko gurfanar da shi a gaban kotu ba, ya samu damar tsayawa takarar shugaban ƙasa.

Diomaye Faye, wanda jama’a ba su san shi sosai ba har zuwa shekara ɗaya da ta gabata, ya samu farin-jininsa ne bayan gallaza wa jam’iyyarsa ta Pastef da aka yi a baya-bayan nan, amma kuma abin da ya fi ɗaga martabarsa shi ne yadda madugun ƴan adawar Senegal Ousmane Sonko ya ce a zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa.

Masu sanya idanu sun bayyana cewa nasarar Diomaye Faye (Da jam’iyyarsa) wata girgizar ƙasa ce ta siyasa kuma za ta sanya a sauya tunani a harkokin siyasar ƙasar.

Faye na kallon kansa a matsayin ɗan takarar kawo sauyi da kishin Afirka baki ɗaya.

Manufofinsa sun haɗa da dawo da martaba da ƙimar Senegal, wadda ya ce an sayar wa ƴan ƙasar waje ita.

Ya kuma yi alƙawarin yaƙar cin hanci da rashawa, tare da raba arzikin ƙasa a tsakanin jama’a.

Faye ya kuma yi alƙawarin sake duba yarjejeniyoyin haƙar ma’adanai, iskar gas da albarkatun man fetur a ƙasar da ta shirya fara haƙo mai da gas a ƙarshen shekarar nan ta 2024.

Ƙasashen duniya sun sanya idanu sosai kan zaɓen na Senegal, wanda ya zo bayan tashin-tashinar siyasa ta tsawon shekara uku a ƙasar da take ɗaya daga mafi zaman lafiya a Afirka.

Senegal ƙasa ce da ta ƙulla alaƙa mai ƙarfi da Yammacin duniya a lokacin da Rasha ke ƙoƙarin ƙara saita kanta a yankin ta hanyar ƙulla ƙawance da ƙasashen Sahel.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like