No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wata ‘yar kasuwa, Anthonia Ubong, a ranar Litinin, ta roƙi wata kotun al’ada da ke zamanta a Jikwoyi, Abuja, da ta yi wa mijinta addu’ar rabuwar aure bisa dalilin rikicin cikin gida.

Anthonia ta gabatar da buƙatar ne a ƙoƙarinta na ƙare ƙarar da mijinta, Mista Ime ya shigar.

Ta ce, “Mijina ba ya ba ni abinci. Ya murguɗa kafata a lokacin da na ce ya ba ni Naira 100 in saya abinci a lokacin ina da ciki wata takwas.

KU KUMA KARANTA: Ta nemi a raba aurenta, saboda rashin soyayya da kulawar mijinta

Ciwon ƙafa na bai daina ba sai da na haihu. “Ya kuma ƙi biyan Naira 60,000 na tiyatar da na yi na haifi jariri bayan na yi naƙuda mai tsawo.

Mama da ƙanwata ne suka biya kuɗi suka kula dani. Naira 4,000 kawai mijina ya ba ni.”

Ta kuma yi zargin cewa mijin nata ya yi mata naushi a fuska tare da raba ƙashinta, inda ta ƙara da cewa ya girme ta da shekara 11 don haka bai yarda ta ce komai ba a auren.

Ta roƙi kotu da ta raba auren ta kuma ba ta riƙon ‘ya ɗaya tilo da ta haifa. Mai shari’a, Misis Thelma Baba, ta ɗage sauraron ƙarar, zuwa ranar 28 ga watan Satumba, domin yi mata tambayoyi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...