Connect with us

Labarai

Soke lasisin dubban kamfanonin canji ba zai kawo maslaha ba – ‘Yan Canji

Published

on

‘Yan kasuwar canjin kuɗi da dama sun nuna rashin gamsuwa da soke lasisin sama da kamfanonin canji 4,000 da babban bankin Najeriya CBN ya yi.

Matakin dai ya ƙara jawo ƙorafi daga masu canjin da ke cikin barazanar fuskantar samamen jami’an tsaro da ke zargin su da tada farashin dala.

Duk da ɗaukar matakin yajin aiki na wuni ɗaya da kasuwar canjin ta yi don barranta kanta da hannu a tashin farashin, hakan bai hana ƙarin matakai masu tsauri kan ‘yan canjin ba.

Alhaji Sani Danmasanin Dogon Daji da ke cikin waɗanda aka soke mu su lasisi, ya ce ya cika ƙa’idojin da su ka dace amma bai tsira daga dirar mikiyar babban bankin ba.

Alhaji Sani ya ce wannan abin da CBN ya yi ya kamata ya tsaya ya yi nazari ya sake dubawa, saboda mutane da yawa sun bi ƙa’idojin da babban bankin ya bayar, amma sunayensu bai fito ba a jerin sunayen da suka fitar.

Shugaban ƙungiyar kasuwar canji ta Abuja, Alhaji Abdullahi Abubakar Dauran, ya ce su na biyaiya ga matakan gwamnati, amma ba su da hannu ko kaɗan a tashin farashin “mu ko nawa dala ta kama za mu yi kasuwancin mu don in ta sauko ma mun fi samun riba.”

KU KUMA KARANTA:Tashin farashin dala na daga cikin manyan matsalolin Najeriya – ƙwararru

Shi kuma shugaban ‘yan arewa mazauna kudu, Ambasada Musa Sa’idu, ya ce ba batun canjin kudi ne ya jefa Najeriya cikin tsada ba; hakan na da nasaba da jibgin bashin da gwamnatin Tinubu ta gada.

Gwamnan babban bankin CBN Olayemi Cardoso, ya dawo da tsarin ba wa ‘yan canji dala don daidaita farashin saɓanin yanda tsohon gwamnan bankin Godwin Emefiele ya dakatar da hulɗa da ‘yan canjin da zargin su da tallafawa almundahana da ƙungiyoyin ta’addanci.

Cardoso ya yi alwashin ɗaukar matakan rage tashin farashi da yanzu ya ke fiye da kashi 29 cikin 100 a Najeriya zuwa kashi 21.4 cikin 100.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like