Ƙasashen Waje
Sojojin Pakistan tara sun mutu, sakamakon hare-haren ‘yan Taliban
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2023/09/Screenshot_20230901-213915_1.jpg)
Wani ɗan kunar baƙin wake ya kashe sojoji tara ta hanyar kutsawa da babur ɗinsa cikin wata motar sojoji a arewa maso yammacin Pakistan.
Wannan dai shi ne hari mafi muni da aka kai wa sojojin a bana, kamar yadda jami’ai suka bayyana a ranar Juma’a.
Wasu sojoji biyar kuma sun jikkata a harin da aka kai cikin dare a gundumar Bannu, wani ƙaramin gari da ke maƙwabtaka da yankin Waziristan da ke kusa da kan iyakar Afghanistan.
Yankin dai ya taɓa riƙe hannun mayaƙan Islama masu alaƙa da ƙungiyar Al-Qaeda.
Sanarwar da sojoji suka fitar a yammacin jiya Alhamis ta ce sojojin sun killace yankin bayan tashin bam ɗin tare da neman waɗanda suka kai harin.
KU KUMA KARANTA: Taliban ta hana matan Afghanistan fita karatu a UAE
Kawo yanzu dai babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin kai waɗannan hare-hare na baya-bayan nan, sai dai ƙungiyar Taliban ta Pakistan da ƙungiyar IS na kai hare-hare kan jami’an tsaro da fararen hula a yankin.
‘Yan Taliban na Pakistan, waɗanda suka rabu da takwarorinsu na Afganistan duk da cewa dukkansu suna bin tsarin Islama mai tsaurin ra’ayi iri ɗaya, sun kashe dubban mutane a irin waɗannan hare-hare a cikin shekarun da suka gabata.
An fatattake su daga yankunan da suke da ƙarfi a kan iyakar Afghanistan a wani jerin hare-hare tun shekara ta 2014.
Sun yi ta neman sake haɗuwa bayan faɗuwar Kabul ga hannun ‘yan Taliban na Afghanistan a 2021.
Ƙasashen Waje
Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali
![Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/IMG_20240704_074342.jpg)
Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali
Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.
Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.
Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.
KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai
Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.
Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.
Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.
Ƙasashen Waje
A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila
![A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/20243475_0-0-5499-3097.jpeg)
A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila
Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.
Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.
KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan
Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.
Ƙasashen Waje
Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan
![Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/20306309_0-402-5000-2817.jpeg)
Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan
Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.
A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”
Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.
Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.
Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.
KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD
Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano