Connect with us

Labarai

Sojojin Najeriya sun lalata haramtattun wurare tace mai 36, sun kama mutane 22 a yankin Neja Delta

Published

on

Hedikwatar tsaro ta ce dakarun ‘Operation Delta Safe’ sun lalata haramtattun wurare tace man fetur 36 tare da kama wasu mutane 22 da ake zargin ɓarayin mai ne a cikin makonni biyu da suka gabata.

Darakta mai kula da ayyukan yaɗa labarai na tsaro, Manjo janar Edward Buba, ya bayyana haka ne a yayin da yake bayar da ƙarin haske kan ayyukan rundunar a wani taron manema labarai na mako biyu a ranar Alhamis a Abuja.

Buba ya ce, sojojin sun kuma lalata ramuka 61, kwale-kwalen katako 32, tankunan ajiya 87, motoci uku, tanda 126 na dafa abinci, injin fita guda uku, jirgin ruwa mai sauri ɗaya, babura biyu, janareta ɗaya da injinan fanfo guda biyu. Ya ce sojojin sun kuma ƙwato litar ɗanyen mai lita 310,700, lita 14,675 na Automotive Gas Oil, lita 49,000 na kananzir Dual Purpose, makami ɗaya da alburusai uku.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Najeriya sun lalata haramtattun hanyoyin tace mai 57, sun kama 16

A cewarsa, “Sojoji a ranar 24 ga watan Yuli, sun kama wani kwale-kwalen katako da ke ɗauke da lita 1000 da ake zargin satar ɗanyen mai ne a yankin Wellhead Cluster Opukushi a ƙaramar hukumar Ekeremor ta jihar Bayelsa.”

A yankin Kudu maso Gabas, dakarun Operation UDO KA sun kai samame kan sansanonin da maɓoyar ‘yan asalin yankin Biafra/Eastern Security Network a jihohin Abiya da Anambara.

Ya ce sojojin sun kuma kama wasu da ake zargin ’yan bindiga ne, tare da kuɓutar da mutanen da aka yi garkuwa da su tare da ƙwato makamai da alburusai a ƙaramar hukumar Onitsha ta Arewa da ke Anambara.

“A yayin gudanar da samamen, sojojin sun ƙwato bindiga ƙirar AK47 guda ɗaya ɗauke da bindigogi 35 na musamman mai nauyin 7.62, bindigogin fanfo guda shida, bindigar gida ɗaya, bindigar ɗane ɗaya, bam ɗin hannu guda ɗaya, motoci huɗu, babura tara, adduna 925. da kuma masu kaifi 151.

“Sauran sun haɗa da sikila 1,080, rigar ‘yan sandan Najeriya da takalma, rigar IPOB/ESN, mai magana ƴaya, rigar ruwan sama da takalmi da sarƙa.

Sojojin sun kuma kama wasu ‘yan bindiga uku tare da kuɓutar da mutane tara da aka yi garkuwa da su.

“Gaba ɗaya, sojoji za su ci gaba da ɗorawa wajen tunkarar ƙalubalen tsaro kuma za su ci gaba da yaƙar masu laifin don miƙa wuya.

“Ana sa ran ’yan Najeriya masu kishin ƙasa za su ci gaba da baiwa sojoji goyon baya, kuma za su tsaya tare da sojoji don fatattakar masu aikata wannan munanan ayyuka daga cikinmu. Tare za mu iya fitar da su,” inji shi.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Sojoji sun kashe ‘yan fashi 10 tare da ceto mutane tara a Zamfara | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Tinubu na shirin zuba tiriliyan 2 don bunƙasa tattalin arziki

Published

on

Tinubu na shirin zuba tiriliyan 2 don bunƙasa tattalin arziki

Tinubu na shirin zuba tiriliyan 2 don bunƙasa tattalin arziki

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya umarci tawagarsa ta tattalin arzikin ƙasar su shirya wani tsari na zuba naira tiriliyan biyu, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 1.33 don magance matsalolin da ake da su game da samar da abinci da hauhauwar farashi da kuma ƙarfafa muhimman sassa, in ji Ministan Kuɗi a ranar Alhamis.

Shirin, wanda za a aiwatar da shi tare da haɗin gwiwar gwamnatocin jihohi da kamfanoni masu zaman kansu, zai ware naira tiriliyan ɗaya, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 664.45 ga harkokin noma da samar da abinci da kuma bangaren makamashi, sai wata naira biliyan 350 domin kula da lafiya da walwalar jama’a, kamar yadda Olawale Edun ya fadawa manema labarai.

Tun bayan hawansa mulki a watan Mayun bara, Tinubu ya aiwatar da sauye-sauye da suka haɗa da rage tallafin man fetur da wutar lantarki da kuma rage darajar Naira sau biyu, a yayin da yake fafutukar ƙara zuba jari da ƙara yawan kayayyakin da ake samarwa.

KU KUMA KARANTA: Ɗangote ya soki sabon tsarin gwamnatin Tinubu

Sai dai tattalin arzikin ƙasar ba ya samun ci gaba cikin sauri ƙasa da 6% a duk shekara kamar yadda ya yi fata, yayin da sauye-sauyen suka sa tashin farashin kayayyaki ya kai mafi muni a cikin shekara 28, ya kuma ta’azzara yanayin rayuwa.

“Abu na farko da shugaban ya mayar da hankali a kai shi ne samar da abinci” a cewar Edun ranar Laraba bayan da Tinubu ya ƙaddamar da wani gyara na tsarin tafiyar da tattalin arziki.

Edun ya ce “Jajircewa wajen samar da abinci a farashi mai rahusa da kuma samar da shi da yawa shi ne abin da Shugaban Ƙasa ya fi mayar da hankali a wannan lokaci.”

Har ila yau, shirin na son magance matsalar raguwar yawan man da ake haƙowa da nufin ƙara yawansa zuwa ganga miliyan biyu a kowace rana, ta yadda za a samar da ƙarin kuɗaɗen shiga da kuma musayar kuɗaɗen waje ga tattalin arzikin ƙasar.

Najeriya ta dogara ne da man fetur wajen samun fiye da rabin kuɗaɗen shigarta da kuma kusan kashi 90% na kuɗin waje.

Sai dai yawan man da ake hakowa ya ragu a shekarun baya-bayan nan, inda satar man da zagon kasa da kuma ficewar manyan kamfanoni daga wuraren da ake haƙo man saboda matsalar rashin tsaro, inda suke mayar da hankali kan binciken mai a teku.

Edun bai fayyace lokacin aiwatar da shirin bunƙasa tattalin arzikin ba.

Continue Reading

Labarai

A fara duban watan sabuwar shekarar Musulunci – Sarkin Musulmi

Published

on

A fara duban watan sabuwar shekarar Musulunci - Sarkin Musulmi

A fara duban watan sabuwar shekarar Musulunci – Sarkin Musulmi

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar ya umarci al’umma da su soma duban watan Muharram na Sabuwar Shekarar musulunci ta 1446 Hijiriyya daga ranar Jumu’a 5 ga watan Yuli, 2024.

A madadin Sarkin Musulmi, Wazirin Sakkwato kuma Shugaban Kwamitin Bayar da Shawara kan Harkokin Addini a Masarautar Sarkin Musulmi, Farfesa Sambo Wali Junaid, ne ya fitar da sanarwar.

Farfesa Sambo, ya ce duk wanda ya samu ganin watan ya sanar da Majalisar Sarkin Musulmi ko wani uban kasa ko hakimi domin sanar da al’umma.

KU KUMA KARANTA: Dole mu kare martabar Sarkin Musulmi – Kashim Shettima

Watan Muharram shi ne watan farko a tsarin watanni 12 na Shekarar musulunci.

Idan an ga watan, Asabar 6 ga watan Yuli, 2024, zai kasance ranar farko a shekarar 1446 Hijiriyya.

Continue Reading

Labarai

‘Yan ta’adda sun kashe mutane sama da mutum 7,000 a Yammacin Afirka a bana – Tuggar

Published

on

‘Yan ta’adda sun kashe mutane sama da mutum 7,000 a Yammacin Afirka a bana - Tuggar

‘Yan ta’adda sun kashe mutane sama da mutum 7,000 a Yammacin Afirka a bana – Tuggar

Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar, ya bayyana buƙatar gaggawa wajen haɗa kai don yaƙi da ta’addanci da sauran matsaloli na rashin tsaro a Yammacin Afirka.

A saƙon da ya wallafa a shafinsa na X, Tuggar ya ce daga watan Janairu zuwa watan Mayun 2024, an samu hare-haren ‘yan ta’adda 800 a Yammacin Afirka, musamman a ƙasashen Burkina Faso, Mali da Nijar.

Ya ƙara da cewa sama da mutane 7,000 ne suka mutu sakamakon hare-haren na ta’addanci a yankin.

KU KUMA KARANTA: Bai kamata ƴan ba-ni-na-iya su shigo da matsalolinsu Gabas ta Tsakiya ba – Turkiyya

“Dole ne mu haɗa kai waje guda don magance matsalolin tsaro, kuma mu yi aiki ba gajiyawa domin tabbatar da tsaro, dimokuraɗiyya da cigaban yankinmu,” in ji Tuggar.

Ya ƙara da cewar a yayin taron, sun kuma sake nazari da duba kan Tsarin Dimokuraɗiyya da Shugabanci na ECOWAS, inda ya kuma yaba da ayyukan samar da zaman lafiya da taimakon jinƙai da ake bayarwa a yankin.

Ƙasashen Yammacin Afirka dai suna fama da hare-hare na ƙungiyoyin da ke da alaƙa da ISIS da Boko Haram ko ISWAP.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like