No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Jami’an tsaron sirri a Burkina Faso sun daƙile yunƙurin juyin mulki da wasu suka yi a ƙasar, a cewar gwamnatin mulkin sojin ƙasar.

Gwamnatin na zargin cewa wasu jami’ai sun shirya kawo ruɗani a ƙasar da kuma jefa ta cikin tashin hankali.

Hakan ya zo ne kasa da shekara guda da karɓe ikon mulkin ƙasar da shugaba Ibrahim Traoré ya yi.

Juyin mulkin da aka yi a ƙasar a 2022, shi ne na biyu da aka samu, a daidai lokacin da ake samun ƙaruwar ayyukan masu iƙirarin jihadi.

Wata sanarwa da hukumomi suka karanta a gidan talabijin ɗin ƙasar da yammacin ranar Laraba, sun ce sun kama wasu mutane, kuma suna ci gaba da neman wasu, sai dai ba su bayar da wani ƙarin bayani ba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...