No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sojojin Isra’ila sun yi awon gaba da Falasɗinawa kusan 300 a ci gaba da kutsawa da suke yi cikin asibitin Al Shifa da ke birnin Gaza.

Wata sanarwa ta ce “sojoji sun kama kusan mutum 300 tare da kawar da ƴan ta’adda da dama.

KU KUMA KARANTA: Blinken zai je Saudiyya da Masar domin tattaunawa kan tsagaita wuta a Gaza

Sojojin sun kai harin ne a ranar Litinin da ta gabata, wanda ke dauke da dubban marasa lafiya da suka jikkata da kuma mazauna wurin.

A shekarar da ta gabata a watan Nuwamba, Isra’ila ta kai hari a asibitin, lamarin da ya tayar da hankalin kasashen duniya.

Tel Aviv ta yi iƙirarin karya cewa mayakan Hamas na amfani da asibitin wajen ayyukan soji. Kwanaki bayan haka ya bayyana a fili cewa sojojin Isra’ila a haƙiƙa suna magana ne a kan tudun da ke ƙarƙashin ginin da Isra’ila ta gina a shekarar 1983 a lokacin da ta yi wa Gaza mummunar mamayar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...