Ƙasashen Waje
Sojojin gwamnatin Habasha sun sake ƙwace ikon birnin Lalibela
Birnin Lalibela a yankin arewa na ƙasar Habasha, ɗaya daga cikin birane dake kumshe da mujamiu ya koma hannun dakarun Gwamnati, rahotanni daga yankin na bayyana cewa mayaƙan sa kai da aka sani da sunan “Fano’ sun fice daga garin cikin dare vayan mamaye gari na wani lokaci.
A baya dai mayakan sa kai sun goyi bayan sojojin Habasha tsawon shekaru biyu na rikici tsakaninta da hukumomin ‘yan tawaye na yankin Tigray, wanda ya kare tare da yarjejeniyar da aka sanya hannu a watan Nuwamba 2022 a Pretoria na ƙasar Afirka ta Kudu.
Sai bai da dama na kallon wannan yarjejeniya a matsayin koma baya ga kawance yayin da ‘yan ƙabilar Amhara ke zaman doya da man ja da mutanen Tigray.
Yarjejeniyar ta ƙara dagula al’amura a yankin na Amhara, wanda ya kawo cikas ga tsarin hukumomin a ɓangaren da ya shafi yunkurin kwance damarar sojojin yankin a watan Afrilu.
KU KUMA KARANTA: Sojoji sun kama masu ƙera haramtattun makamai a Filato
Tsawon wani lokaci kafin wayewar gari,mayaka yan sa kai da aka sani da Fano ne ke riƙe da mafi yawan garuruwan, sun haɗa karfi da sauren mayaƙa wajen barin garin,” in ji wani mazaunin garin wanda shi ma ya nemi a sakaya sunansa saboda dalilan tsaro.
A ranar Laraba da yamma wasu mazauna yankin sun nuna cewa mayaƙan sa kai na ƙungiyar Fano ne ke iko da mafi yawan Lalibela kuma an sake tura dakarun gwamnatin tarayya zuwa wajen wani sansani da ke gefen garin.
Ƙasa ta biyu mafi yawan jama’a a Afirka da kusan mutane miliyan 120, Habasha, ƙasa da kusan kabilu 80, ta shiga rikici wanda ya daidaita ƙasar da kuma haifar da yan gudun hijira da dama.
Ƙasashen Waje
Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali
Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali
Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.
Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.
Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.
KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai
Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.
Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.
Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.
Ƙasashen Waje
A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila
A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila
Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.
Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.
KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan
Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.
Ƙasashen Waje
Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan
Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan
Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.
A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”
Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.
Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.
Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.
KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD
Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano