Connect with us

Ƙasashen Waje

Sojoji sun roƙi kotun ECOWAS ta tilasta wa makwabtan Nijar ɗage takunkumai

Published

on

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta buƙaci Kotun Afirka ta Yamma ta ECOWAS da ta ba da umarnin ɗage takunkuman da maƙwabtanta suka ƙaƙaba wa ƙasar sakamakon juyin mulkin da aka yi a watan Yuli, inda aka hamɓarar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar.

“Babu wani ɓangare na al’ummar Nijar da waɗannan takunkuman ba su shafa ba” waɗanda suka janyo wahalhalu na tattalin arziki a daya daga cikin ƙasashen mafi talauci a duniya, a cewar Youkaila Yaye, ɗaya daga cikin lauyoyin gwamnatin mulkin sojan, yayin da yake yi wa kotun jawabi a zaman da aka yi a ranar Talata a Abuja, babban birnin Najeriya.

Bayan da manyan sojoji suka hamɓarar da shugaban ƙasar Nijar Mohamed Bazoum, ƙasar ta fuskanci takunkuman tattalin arziki daga ƙungiyar ECOWAS da kuma wasu ƙasashen da suka haɗa da Amurka da suke bayar da agajin kiwon lafiya da tsaro da kayayyakin more rayuwa.

KU KUMA KARANTA: An rantsar da mambobin hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijar

Makwabtan kasashe sun rufe iyakokinsu da Nijar kuma an katse sama da kashi 70 na wutar lantarkinta, wacce Najeriya ke bayarwa, bayan dakatar da hada-hadar kuɗaɗe da ƙasashen Yammacin Afirka.

An rufe ƙadarorin Nijar a bankunan ƙasashen waje tare da hana ɗaruruwan miliyoyin daloli na agaji.

Takunkuman su ne mafi tsauri da ƙungiyar ƙasashen yankin ta ƙaƙaba wa ƙasar, a yunƙurin da take yi na daƙile juyin mulki a yankin Sahel na Afirka mai fama da rikici.

Sai dai ba su yi wani tasiri ko kaɗan ba wajen rage burin gwamnatin mulkin sojan, wadda ta ci gaba da nuna ƙarfin ikonta yayin da miliyoyin mutane a Nijar ke fuskantar ƙunci.

A yayin zaman kotun, lauyoyin gwamnatin sun bayyana yadda takunkuman ke cutar da Nijar: Yara ba sa iya komawa makaranta saboda ƙarancin kayayyaki. Kayayyaki na ƙarewa a shagunan sayar da magunguna. Harkokin kasuwancin sun tsaya cak saboda tsadar kayayyaki.

Yaye ya zargi ECOWAS da ladabtar da ‘yan Nijar kan juyin mulkin ta hanya mai tsauri fiye da yadda ta yi ga wasu ƙasashen da aka yi juyin mulki, “musamman dangane da hada-hadar kuɗi.

Gwamnatin mulkin sojin ta buƙaci kotun da ta sassauta takunkuman har sai an yanke hukunci. Sai dai ECOWAS ta nuna rashin amincewa da buƙatar tasu.

Lauyan ECOWAS, Francois Kanga-Penond, ya ce ba a amince da gwamnatin mulkin soja a ƙarƙashin tsarin ƙungiyar ba kuma ba ta da ikon shigar da irin wannan ƙara a kotu.

Kotun ta ɗage zaman har zuwa ranar 7 ga watan Disamba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like