No menu items!

Sample Page Title

Date:

Dakarun sojin Najeriya sun kashe mayaƙan ISWAP shida tare da fatattakar wasu da dama a wani harin kwantan ɓauna da ƙungiyar ta kai musu suna sintiri a unguwar Binduldul da ke kan hanyar Maiduguri-Gubio-Kareto-Damasak.

Sojojin da aka girke a Damasak sun yi musayar wuta da ’yan ta’addan suka tsere cikin daji, kamar yadda wata majiyar leƙen asiri ta shaida wa Zagazola Makama, wani mai sharhi kan harkokin tsaro kuma ƙwararre kan yaƙi da ta’addanci a yankin tafkin Chadi.

KU KUMA KARANTA: Sojoji sun kashe ‘yan fashi 10 tare da ceto mutane tara a Zamfara

Majiyar ta ƙara da cewa, sojojin sun shiga cikin dajin domin fatattakar ’yan ta’addar, kuma a yayin arangamar mayaƙan ISWAP da ba a tantance adadinsu ba sun samu raunuka.

Sojoji 3 ne suka samu raunuka a yayin arangamar, yayin da aka ƙwato bindigogin PKT guda biyu, AK-47 guda biyar, da motar bus ƙirar Hummer guda ɗaya da ’yan ta’addar ke amfani da su.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...