Labarai
Sojoji sun ce sun ceto mutum 40 daga hannun ‘yan bindiga a Zamfara
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2023/07/IMG-20230719-WA0023.jpg)
Daga Ibraheem El-Tafseer
Dakarun sojin Najeriya sun ce sun ceto mutum 40 da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a jihar Zamfara.
Dakarun da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Hadarin Daji sun samu nasarar ceto mutanen ne a ƙaramar hukumar Bukkuyum na jihar.
Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa sojojin sun samu nasarar ce bayan samun bayanan sirri da ke cewa ‘yan bindigar sun yi garkuwa da mutanen da ba a san adadinsu ba a ƙauyen Kyairu da Alkama da ke ƙaramar hukumar ta Bukkuyum.
Bayan nan ne sojojin suka tasamma garin da nufin kai samame domin ƙwato mutanen da ke hannun ‘yan bindigar a ranar Talata.
KU KUMA KARANTA: Ku ba mu dama mu kakkaɓe ‘yan ta’adda – sojojin Najeriya ga gwamnonin arewa
Sai dai sojojin sun yi bata-kashi da ‘yan bindigar na wasu sa’o’i kafin su fi ƙarfinsu da tilasta musu tserewa da kuma barin mutanen da suka yi garkuwa da su.
Mutanen da aka ceto ɗin da suka kai 40 tuni suka haɗu da iyalansu yayin da aka miƙa goma daga cikinsu kuma ga hannun Sarkin Gwashi domin haɗa su da iyalansu.
Labarai
Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin
![Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/06/IMG_9713-1.png)
Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin
Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya amince da naɗin sabbin sakatarorin dindindin na gwamnatin tarayya guda takwas da za su cike guraben da ake da su a wasu jihohi da shiyyoyin ƙasar a ma’aikatan gwamnati.
Ajuri Ngelale, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da bayanai ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a jiya Juma’a, inda ya ce an naɗa sabbin sakatarorin dindindin ɗin ne bayan da ofishin shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya ya gudanar da aikin zaɓo su.
KU KUMA KARANTA:Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3
Sakatarorin su ne: Dr Emanso Umobong Okop – Akwa-Ibom, Obi Emeka Vitalis – Anambra, Mahmood Fatima Sugra Tabi’a – Bauchi, Danjuma Mohammed Sanusi – Jigawa, Olusanya Olubunmi – Ondo, Dr Keshinro Maryam Ismaila – Zamfara, Akujobi Chinyere Ijeoma (Kudu-maso-Gabas)) da kuma Isokpunwu Christopher Osaruwamwen (Kudu-maso-Kudu).
“Shugaban ya yi hasashen cewa sabbin sakatarorin dindindin na gwamnatin tarayya za su yi aiki da ƙwazo, himma da riƙon amana ga ƙasa wajen gudanar da ayyukansu tare da tabbatar da ingantacciyar hidima ga al’ummar Najeriya,” in ji sanarwar.
Labarai
Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3
![Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/06/IMG_9717.png)
Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ba da Naira dubu hamsin-hamsin ga iyalai miliyan 3.6 har tsawon wata uku a faɗin Nijeriya.
Wannan na ɗaya daga cikin yarjejeniyoyi da aka cimma a ganawar da Tinubu ya yi da gwamnonin jihohi 36 na ƙasar nan a yau Alhamis a Abuja.
Shugaban ya ba da umarnin raba kuɗin ga iyalai dubu 100 a kowace jiha har na tsawon watanni uku.
Sauran batutuwa da aka cimma a ganawar sun haɗa da:
* Bawa iyalai 100,000 a kowace jiha tallafin N50,000 na tsahon wata uku.
* Ware Naira biliyan 155 domin siyen kayan abinci da za a tallafawa masu ƙaramin ƙarfi kan farashi mai rahusa.
* Baiwa kowace jiha Naira biliyan 10 domin sayen motocin sufuri masu aiki da iska gas domin sauko da farashin kuɗin zirga-zirga.
KU KUMA KARANTA:Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa
* Gaggauta fara aikin hanyar da ta tashi daga Sakkwato zuwa Badagary a Lagos. Hanyar zata ratsa ƙauyuka kimanin 216, madatsun ruwa (dams) guda 58, ƙananan hukumomi 156 da manyan garuruwa 39 da kuma gonaki da suka kai kimanin hectare miliyan ɗaya. Titin zai ratsa jihohin Sokoto da Kebbi da Niger da Kwara da Oyo da Ogun da kuma Lagos.
* Shugaba Tinubu ya kuma amince da biyan kuɗin aikin hanyar jirgin ƙasa daga Fatakwal zuwa Maiduguri wadda za ta ratsa jihohin Rivers da Abia da Enugu da Benue da Nasarawa da Plateau da Bauchi da Gombe da Yobe da kuma Borno.
* Haka nan an amince da biyan kuɗin da ake buƙatar domin yin aikin hanyar jirgin ƙasa da ta taso daga Ibadan zuwa Abuja a wani ɓangare na aikin dogo da ya tashi daga Lagos zuwa Kano. Aikin zai haɗa jihohin Lagos da Ogun da Oyo da Osun da Kwara da Niger da Abuja da Kaduna da kuma Kano.
* Shugaban ƙasa ya kuma bada umarnin cigaba da aikin hanyar Lagos zuwa Calabar wadda kuma zata yi rassa a jihohin Benue da Kogi da Abuja da Nasarawa da Enugu da Ebonyi.
Labarai
Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa
![Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/06/IMG_9714.png)
Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa
Gwamnatin jihar Kano ta yi watsi da batun ɗaga tutar masarauta da aka yi a gidan sarki na Nassarawa wurin da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ke zaune, inda ta bayyana hakan da ƙoƙarin jan hankalin jama’a kawai.
Tutar, wata alama ce ta iko dake nuni da cewar Sarki na nan, a kullum ana ɗaga ta da misalin ƙarfe 6 na safe a kuma sauƙe ta da misalin ƙarfe 6 na yamma. Duk lokacin da sarki ba ya cikin fada ko ya yi balaguro za ta kasance a sauƙe.
Da safiyar ranar Alhamis, aka lura cewar an ɗaga tutar da misalin ƙarfe 6 na safiya a fadar Nassarawa, abin da ya haifar da kace-nace dama raɗe-raɗi.
Kowane daga cikin Aminu Ado Bayero da Muhammadu Sanusi II na iƙirarin shi ne Sarkin Kano kuma suna ci gaba da aiwatar da ayyukan sarauta.
KU KUMA KARANTA:An sauya Kwamishinan ’yan sandan Kano
Gwamnatin jihar ce ta sauƙe Aminu Ado Bayero tare da sake naɗa Muhammadu Sanusi biyo bayan yiwa dokar masarautu ta Kano kwaskwarima.
An ɗaga irin wannan tuta a fadar gidan Rumfa, inda Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ke zaune.
Mai magana da yawun gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya yi fatali da batun ɗaga tuta a fadar Nassarawar, inda yace hakan wani yunƙuri ne na jan hankalin al’umma.
Ya shaidawa manema labarai cewar, “hakan wani yunƙuri ne na jan hankalin al’umma. Amma babu shakku ko tantamar cewar Sanusi ne Sarkin Kano.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano
Pingback: Gwamna Sani ya yabawa sojojin da suka kawar da masu tayar da ƙayar baya a Kaduna | Neptune Prime Hausa
Pingback: ‘Yan bindiga sun sace matafiya a Edo | Neptune Prime Hausa