Connect with us

Labarai

Sojoji sun ƙuɓutar da ɗaliban jami’a shida waɗanda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a Zamfara

Published

on

An ƙuɓutar da ɗalibai shida daga cikin ɗalibai 24 na Jami’ar Tarayya da ke Gusau a Jihar Zamfara waɗanda aka yi garkuwa da su da sanyin safiyar ranar Juma’a, kamar yadda jaridar News Point Nigeria ta ruwaito.

Wata majiya mai ƙarfi na soji na kusa da Kwamandan Birged 1 na Sojojin Najeriya Gusau, ta tabbatar wa da wakilinmu hakan, biyo bayan farmaƙin da ‘yan bindiga suka kai a yankin Sabon-Gida da ke ƙaramar hukumar Bunguɗu.

Ya ce a halin yanzu Kwamandan Birgediya Birgediya Janar Sani Ahmed ne ke jagorantar aikin tare da sauran jami’an tsaro a dajin da ke ƙaramar hukumar Tsafe a jihar.

Majiyar ta kuma tabbatar da cewa an kashe ‘yan ta’adda da dama a farmaƙin da ake kai tare da ƙwato wasu makamai.

KU KUMA KARANTA: Bayan biyan miliyan biyar, ‘yan bindiga sun saki ɗaya daga cikin masu yiwa ƙasa hidima da aka yi garkuwa da su a Zamfara

Tun da farko, wani ɗalibin makarantar, wanda ya nemi a sakaya sunansa saboda dalilai na tsaro, ya shaida wa ‘News Point Nigeria’  cewa an sace ‘yan makarantar sama da 24, galibinsu mata yayin harin.

Wani mazaunin unguwar Sabon-Gida mai suna Nazeer Sabon-Gida ya kuma tabbatar da cewa ‘yan bindigar sun mamaye al’ummar garin ne da misalin ƙarfe uku na safe inda suka fara harbe-harbe ba gaira ba dalili.

A cewarsa, an kai hari a ɗakunan kwanan ɗalibai uku, kuma ‘yan bindigar sun tafi da dukkan ɗaliban da ke cikin ɗakunan kwanan.

A wani labarin kuma, rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta tabbatar da sace ɗaliban.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, ASP Yazid Abubakar, a wata tattaunawa ta wayar tarho ranar Juma’a, ya ce har yanzu rundunar ba ta tabbatar da adadin ɗaliban da aka sace ba.

Ya kuma tabbatar da cewa ana ci gaba da aikin ceto.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Gwamna Lawal ya yi taron gaggawa da shugabannin hukumomin tsaro a jihar | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da likita a Kogi | Neptune Prime Hausa

  3. Pingback: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da likita a Kogi - LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like