No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban Tinubu ya rattaba hannu kan dokar Haraji

Daga Jameel Lawan Yakasai

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya sanya hannu kan dokokin gyaran haraji guda huɗu da suka samu amincewar majalisun dokoki na tarayya, a wani mataki da ake ganin zai sauya tsarin haraji da tattalin arzikin ƙasar gaba ɗaya.

KU KUMA KARANTA:Majalisar wakilai a Najeriya, ta amince da ƙudirin dokar haraji a ƙasar

Bikin sanya hannun ya samu halartar shugaban majalisar dattawa, kakakin majalisar wakilai, shugabannin kwamitocin kudi na majalisu, shugaban kungiyar gwamnoni, ministan kudi da kuma babban lauya na ƙasa.

Dokokin da aka sanyawa hannu sun haɗa da Kudurin Dokar Haraji na Najeriya, Kudurin Dokar Gudanar da Haraji, Kudurin Kafa Hukumar Tara Haraji ta Najeriya, da Kudurin Kafa Hukumar Haɗin Gwiwar Tara Haraji.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...