Connect with us

Ƙasashen Waje

Shugaban Senegal, Sall, ya kare matakinsa na ɗaga zaɓen ƙasar

Published

on

Shugaban Senegal Macky Sall ya kare matakinsa na ɗaga zaɓen ƙasar bayan zanga-zangar da ta ɓarke a ƙasar a ranar Juma’a a ƙasar.

A wata tattaunawa da aka yi da shi a karon farko bayan ɗaga zaɓen, Sall ya yi watsi da zarge-zargen da ake yi kan cewa matakin da ya ɗauka ya saɓa wa shari’a.

Ya bayyana cewa ƙasar na buƙatar ƙarin lokaci domin magance matsalolin da take fuskanta kan cire sunayen wasu ƴan takara saboda rashin cancanta da kuma rikicin da ake yi tsakanin ɓangaren majalisa da kuma na shari’a.

Senegal na daga cikin ƙasashen Yammacin Afirka da ke da dimokuraɗiyya wadda ke tsaye da gindinta, sai dai a halin yanzu dimokuraɗiyyar ƙasar na cikin barazana tun bayan sanarwar ɗaga zaɓen.

KU KUMA KARANTA: ECOWAS ta buƙaci hukumomin Senegal su sanya ranar gudanar da zaɓe

Macky Sall ya musanta cewa yana so ya ci gaba da mulki a ƙasar. “Babu abin da nake nema baya ga na bar ƙasar cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali,” kamar yadda Sall ya bayyana.

“ A shirye nake na miƙa mulki. A shirye nake da hakan a kullum.” Sall ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AP cewa a cikin fadar shugaban ƙasar da ke Dakar, a lokacn da yake waje, ɗaruruwan mutane sun fito kan tituna inda suke ƙona tayoyi da jefa duwatsu.

Aƙalla ɗalibi ɗaya aka kashe a makaranta bayan da aka yi zanga-zanga a birnin Saint Louis da ke arewacin kasar, kamar yadda wata sanarwa daga mai shigar da ƙara na ƙasar ta bayyana.

“Makomarmu na cikin wani hali,” in ji Mohamed Sene, mai shigar da ƙara a Dakar.

Sall wanda ya hau kan karagar mulki a shekara ta 2012 kuma yana shirin kammala wa’adinsa na biyu a ranar 2 ga watan Afrilu, inda ya dage zaben da aka shirya yi a ranar 25 ga watan Fabrairu a daidai lokacin da ake shirin fara yakin neman zabe.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like