Connect with us

Ƙasashen Waje

Shugaban Senegal, Sall, ya kare matakinsa na ɗaga zaɓen ƙasar

Published

on

Shugaban Senegal Macky Sall ya kare matakinsa na ɗaga zaɓen ƙasar bayan zanga-zangar da ta ɓarke a ƙasar a ranar Juma’a a ƙasar.

A wata tattaunawa da aka yi da shi a karon farko bayan ɗaga zaɓen, Sall ya yi watsi da zarge-zargen da ake yi kan cewa matakin da ya ɗauka ya saɓa wa shari’a.

Ya bayyana cewa ƙasar na buƙatar ƙarin lokaci domin magance matsalolin da take fuskanta kan cire sunayen wasu ƴan takara saboda rashin cancanta da kuma rikicin da ake yi tsakanin ɓangaren majalisa da kuma na shari’a.

Senegal na daga cikin ƙasashen Yammacin Afirka da ke da dimokuraɗiyya wadda ke tsaye da gindinta, sai dai a halin yanzu dimokuraɗiyyar ƙasar na cikin barazana tun bayan sanarwar ɗaga zaɓen.

KU KUMA KARANTA: ECOWAS ta buƙaci hukumomin Senegal su sanya ranar gudanar da zaɓe

Macky Sall ya musanta cewa yana so ya ci gaba da mulki a ƙasar. “Babu abin da nake nema baya ga na bar ƙasar cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali,” kamar yadda Sall ya bayyana.

“ A shirye nake na miƙa mulki. A shirye nake da hakan a kullum.” Sall ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AP cewa a cikin fadar shugaban ƙasar da ke Dakar, a lokacn da yake waje, ɗaruruwan mutane sun fito kan tituna inda suke ƙona tayoyi da jefa duwatsu.

Aƙalla ɗalibi ɗaya aka kashe a makaranta bayan da aka yi zanga-zanga a birnin Saint Louis da ke arewacin kasar, kamar yadda wata sanarwa daga mai shigar da ƙara na ƙasar ta bayyana.

“Makomarmu na cikin wani hali,” in ji Mohamed Sene, mai shigar da ƙara a Dakar.

Sall wanda ya hau kan karagar mulki a shekara ta 2012 kuma yana shirin kammala wa’adinsa na biyu a ranar 2 ga watan Afrilu, inda ya dage zaben da aka shirya yi a ranar 25 ga watan Fabrairu a daidai lokacin da ake shirin fara yakin neman zabe.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Published

on

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Daga Ibraheem El-Tafseer

Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.

A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.

A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.

KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Published

on

Isra'ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza, inda ta tilasta wa ɗaruruwan Falasɗinawa tserewa bayan da soji suka kuma ba da umarnin ƙaurace wasu yankuna masu yawan jama’a.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Isra’ila sun ce an yi musayar wuta da dakarun Masar

Waɗanda suka shaida lamarin sun ce an kai hari da dama a ciki da wajen birnin Khan Younis, inda aka hallaka mutane takwas kuma mutane sama da 30 suka samu raunuka, cewar wata majiyar lafiya da kuma ƙungiyar Red Crescent ta Falasɗinawa.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Published

on

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana - COPEC

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Man Fetur a Ghana ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a samun ƙarin farashin man fetur a ƙasar a farkon watan Yulin 2024.

Ƙungiyar ta Chamber for Petroleum Consumers (COPEC) ta ce akwai alamu masu ƙarfi da ke nuna cewa farashin fetur da man dizel da gas zai ƙaru baki ɗaya a gidajen man da ke faɗin ƙasar, kamar yadda kamfanin watsa labarai na ƙasar Ghana ya ruwaito.

COPEC ɗin ta ce za a samu ƙarin farashin ne sakamakon yadda farashin Cedi ɗin a ƙasar ke ƙara karewa idan aka kwatanta da dalar Amurka.

COPEC ɗin ta yi hasashen cewa farashin man fetur ɗin wanda za a rinƙa sayarwa a gidan mai zai ƙaru da kashi 2.17 cikin 100, wanda hakan ke nufin zai ƙaru daga Cedi 14.17 zuwa Cedi 15.20 a duk lita.

Sai kuma farashin dizel ana sa ran ya ƙaru zuwa 15.21 a kowace lita ɗaya, sai kuma na gas ya koma tsakanin Cedi 13.24 zuwa Cedi 14.64 a duk kilo ɗaya.

KU KUMA KARANTA: Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya

Ƙungiyar ta COPEC ta bayar da shawara ga gwamnatin Ghana da ta yi duk mai yiwuwa domin rage harajin da yake a kan gas ko kuma yin tallafi a farashinsa domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su same shi a farashi mai rahusa.

Ta kuma yi ƙira ga gwamnati da kada ta yi ƙasa a gwiwa wajen dawo da matatar mai ta Tema a kan aiki (TOR) don kaucewa ko kuma rage shigo tattacen man fetur wanda a wani lokacin ake samun gurɓatacce.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like