Shugaban rundunar Sojin ƙasa Lagbaja bai mutu ba – Rundunar Sojin Najeriya

0
27
Shugaban rundunar Sojin ƙasa Lagbaja bai mutu ba - Rundunar Sojin Najeriya

Shugaban rundunar Sojin ƙasa Lagbaja bai mutu ba – Rundunar Sojin Najeriya

Daga Ibraheem El-Tafseer

Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya a ranar Lahadi ta ƙaryata raɗe-raɗin da ake yi cewa Shugaban Rundunar Sojin Ƙasa, COAS, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja ya mutu.

PRNigeria ta rawaito cewa rundunar, a shafin ta na X ta bayyana rahoton a matsayin ƙarya, amma ba ta ba da wani ƙarin bayani ba.

Sai dai kuma a wata sanarwa da Kakakin rundunar, Manjo-Janar Onyema Nwachukwu ya fitar a ranar Asabar, Lagbaja ya tafi hutu ne da kuma duba lafiyar sa a ƙasar waje.

KU KUMA KARANTA: Ba mu da niyyar kafa sansanin soji a Najeriya – Amurka

Ya kuma nuna cewa babu wani giɓi na shugabanci a runudunar sakamakon tafiyar COAS ɗin, inda ya baiyana cewa tuni shugaban sashen manufofi da tsare-tsare na rundunar, Manjo-Janar Abdulsalami Bagudu Ibrahim ya maye gurbin sa kafin ya dawo.

Leave a Reply