Connect with us

Labarai

Shugaban NILEST ya baiwa gwamnatin Najeriya shawara kan yadda za a farfaɗo da masana’antu a ƙasa baki ɗaya

Published

on

Daga Idris Umar, Zariya

Babban Darakta kuma shugaban Cibiyar kimiyyar Fata ta Najeriya (NILEST) dake Samaru Zariya, Farfesa Yakubu ya yi ƙira ga masu ruwa da tsaki, tare da masu bincike, musamman masana’antu, masu saka hannun jari, a ma’aikatun gwamnati da saura cibiyoyi masu zaman kansu da ke Zariya da su zo don samar da wata hanya ta haɗin guiwa da za a samu ci gaba a masana’antun dake faɗin jihar Kaduna musamman ƙasar Zazzau a halin yanzu.

Babban daraktan ya bayyana hakan ne a jawabinsa na ƙarƙare taron kasuwanci da saka hannun jari na ƙasa da (ZANETIS) ta shirya a ranar Asabar a filin Polo dake GRA Zariya ƙaramar hukumar Sabon Gari.

Farfesan ya ƙara da cewa, taron an shirya shi ne domin baje kolin zuba hannun jari a harkar noma da ayyukan haɗin guiwa a kimiyanci don samun fahimta lamarin cikin sauƙi.

Shugaban ya tabbatar da cewa lokaci ya wuce na dogara da satifiket kaɗai a ɓangaren neman abinci.

Kuma ya nuna cewa wannan taron ya na ƙira ne ga dukkan al’umma da su fito don tarbar nazarce-nazarce, don bunƙasa kaifin basirarsu da Allah ya basu kuma su kasance cikin shirin yin gogayya da sauran ƙasashen duniya wajan amfani da ilimin kimiya.

KU KUMA KARANTA: Hamas ta amince da shawarar Qatar da Masar ta tsagaita wuta a Gaza na — Haniya

Shugaban ya yi tambaya kamar haka, Shin wanene ya mallaki biranenmu da suka yi fice ta fuskacin kasuwanci a halin yanzu?

Kuma ya amsa kamar haka “Tabbas, ba waɗanda suka fi kowa yawan satifiket ɗin karatu bane”

Yace ɗaya daga cikin manufofin wannan taron shi ne gwama karatu da kuma ƙwarewa, bincike tare da bunƙasa kasuwanci da aiki tuƙuru don kawo ci gaban ƙasa.

Mai Martaba Sarkin Zazzau Dakta Ahmed Nuhu Bamalli wanda Hakimin ƙasar Gubuchi, Alhaji Dakta Bello Lawal ya wakilce shi tuni Hakimin ya yi alƙawarin bai wa taron duk wata haɗin kai da suke da buƙata wajen ganin manufarsu ya kai gacci.

Masana’antu da manyan cibiyoyi da dama ne dake Zariya da kewaye suka halarci taron na kwanaki goma.

Kuma tabbas kamfanoni masu ƙaramin ƙarfi sun yabawa wanda suka shirya taron.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like