No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Kano KAROTA ta ce ya zama wajibi ta ɗauki matakin fitar da ɓata-garin cikinta domin inganta ayyukan hukumar.

Alfijir Labarai ta rawaito Shugaban Hukumar Karota Engr. Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana haka a wannan rana ta Alhamis lokacin da ya bayar da umarnin tsare wasu Jami’in KAROTA waɗanda ake zargi su da matsawa direbobin mota da karɓe-karɓen kuɗi a wajen su.

Yace hukumar baza ta zuba ido ta bari a sauke tsarin da aka kafa hukumar a kai ba, a don haka ya zama wajibi a hukunta duk wanda aka samu da sauya salon aikin hukumar.

KU KUMA KARANTA: Hukumar KAROTA ta cafke wasu matasa da tarin kayan maye da makamai a Kano

Yaja hankalin direbobin mota da su guji bawa jami’in hukumar ta KAROTA cin-hanci domin baya daga cikin manufar kafa Hukumar.

Ya kuma ƙara da cewa abinda ake buƙata a wajen kowanne direba ya shi ne tabbatar ya mallaki dukkan takardun tuƙi kafin ya hau kan titi, da kuma bin dokokin hanya a lokacin da ake tuƙin.

Daga karshe shugaban ya godewa wasu daga cikin Jami’in Hukumar bisa namijin kokarin da suke yi wajen aiki tukuru tare da tsare mutuncin ayyukan Hukumar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...